< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
It is a good thing to give thanks unto Yhwh, and to sing praises unto thy name, O most High:
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
To shew forth thy lovingkindness in the morning, and thy faithfulness every night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
Upon an instrument of ten strings, and upon the psaltery; upon the harp with a solemn sound.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For thou, Yhwh, hast made me glad through thy work: I will triumph in the works of thy hands.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
O Yhwh, how great are thy works! and thy thoughts are very deep.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A brutish man knoweth not; neither doth a fool understand this.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the wicked spring as the grass, and when all the workers of iniquity do flourish; it is that they shall be destroyed for ever:
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But thou, Yhwh, art most high for evermore.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For, lo, thine enemies, O Yhwh, for, lo, thine enemies shall perish; all the workers of iniquity shall be scattered.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
But my horn shalt thou exalt like the horn of an unicorn: I shall be anointed with fresh oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Mine eye also shall see my desire on mine enemies, and mine ears shall hear my desire of the wicked that rise up against me.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous shall flourish like the palm tree: he shall grow like a cedar in Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Those that be planted in the house of Yhwh shall flourish in the courts of our God.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
They shall still bring forth fruit in old age; they shall be fat and flourishing;
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
To shew that Yhwh is upright: he is my rock, and there is no unrighteousness in him.

< Zabura 92 >