< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A Psalm of a Song for the Sabbath-day. It is a good thing to give thanks to the Lord, and to sing praises to thy name, O thou Most High;
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
to proclaim thy mercy in the morning, and thy truth by night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
on a psaltery of ten strings, with a song on the harp.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For thou, O Lord, hast made me glad with thy work: and in the operations of thy hands will I exult.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
How have thy works been magnified, O Lord! thy thoughts are very deep.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A foolish man will not know, and a senseless man will not understand this.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the sinners spring up as the grass, and all the workers of iniquity have watched; [it is] that they may be utterly destroyed for ever.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But thou, O Lord, art most high for ever.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For, behold, thine enemies shall perish; and all the workers of iniquity shall be scattered.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
But my horn shall be exalted [as the horn] of a unicorn; and mine old age with rich mercy.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
And mine eye has seen mine enemies, and mine ear shall hear the wicked that rise up against me.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous shall flourish as a palm-tree: he shall be increased as the cedar in Libanus.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
They that are planted in the house of the Lord shall flourish in the courts of our God.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Then shall they be increased in a fine old age; and they shall be prosperous; that they may declare
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
that the Lord my God is righteous, and there is no iniquity in him.

< Zabura 92 >