< Zabura 91 >

1 Shi wanda yake zama a wurin Mafi Ɗaukaka zai huta a cikin inuwar Maɗaukaki.
Yeye akaaye mahali pa salama pake Yeye Aliye Juu Sana, atadumu katika uvuli wake Mwenyezi.
2 Zan ce game da Ubangiji, “Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda nake dogara.”
Nitasema kumhusu Bwana, “Yeye ndiye kimbilio langu na ngome yangu, Mungu wangu, ambaye ninamtumaini.”
3 Tabbatacce zai cece ka daga tarkon mai farauta da kuma daga cututtuka masu kisa.
Hakika yeye ataniokoa na mtego wa mwindaji, na maradhi ya kuambukiza ya kuua.
4 Zai rufe ka da fikafikansa, a ƙarƙashin fikafikansa kuwa za ka sami mafaka; amincinsa zai zama maka garkuwa da katanga.
Atakufunika kwa manyoya yake, chini ya mbawa zake utapata kimbilio, uaminifu wake utakuwa ngao na kinga yako.
5 Ba za ka ji tsoron razanar dare, ko kibiyoyi da suke firiya da rana ba,
Hutaogopa vitisho vya usiku, wala mshale urukao mchana,
6 ko bala’in da yake aukowa cikin duhu, ko annobar da take hallakarwa da tsakar rana.
wala maradhi ya kuambukiza yanayonyemelea gizani, wala tauni iharibuyo adhuhuri.
7 Dubu za su iya fāɗuwa a gefenka, dubu goma a hannun damanka, amma ba abin da zai zo kusa da kai.
Ijapo watu elfu wataangukia kando yako, kumi elfu mkono wako wa kuume, lakini haitakukaribia wewe.
8 Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.
Utatazama tu kwa macho yako na kuona adhabu ya waovu.
9 In ka mai da Mafi Ɗaukaka wurin zamanka, har ma Ubangiji wanda yake mafakata,
Kama ukimfanya Aliye Juu Sana kuwa makao yako: naam, Bwana ambaye ni kimbilio langu,
10 to, babu wani mugun abin da zai same ka, ba masifar da za tă zo kusa da tentinka.
basi hakuna madhara yatakayokupata wewe, hakuna maafa yataikaribia hema yako.
11 Gama zai umarci mala’ikunsa game da kai don su tsare ka a dukan hanyoyinka;
Kwa kuwa atawaagiza malaika zake kwa ajili yako, wakulinde katika njia zako zote.
12 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.
Mikononi mwao watakuinua, ili usijikwae mguu wako kwenye jiwe.
13 Za ka taka zaki da gamsheƙa; za ka tattake babban zaki da maciji.
Utawakanyaga simba na nyoka wakali, simba mkubwa na nyoka utawaponda kwa miguu.
14 Ubangiji ya ce, “Domin ya ƙaunace ni, zan kuɓutar da shi; zan kiyaye shi, gama ya yarda da sunana.
Bwana asema, “Kwa kuwa ananipenda, nitamwokoa; nitamlinda, kwa kuwa analikiri Jina langu.
15 Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
Ataniita, nami nitamjibu; nitakuwa pamoja naye katika taabu, nitamwokoa na kumheshimu.
16 Da tsawon rai zan ƙosar da shi in kuma nuna masa cetona.”
Kwa siku nyingi nitamshibisha na kumwonyesha wokovu wangu.”

< Zabura 91 >