< Zabura 91 >
1 Shi wanda yake zama a wurin Mafi Ɗaukaka zai huta a cikin inuwar Maɗaukaki.
El que mora al abrigo del ʼElyón Morará bajo la sombra del Shadday.
2 Zan ce game da Ubangiji, “Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda nake dogara.”
Diré yo a Yavé: ¡Refugio mío y Fortaleza mía, Mi ʼElohim, en Quien confío!
3 Tabbatacce zai cece ka daga tarkon mai farauta da kuma daga cututtuka masu kisa.
Él te librará de la trampa del cazador, Y de la mortal pestilencia.
4 Zai rufe ka da fikafikansa, a ƙarƙashin fikafikansa kuwa za ka sami mafaka; amincinsa zai zama maka garkuwa da katanga.
Con sus plumas te cubrirá, Y debajo de sus alas te refugiarás. Escudo y adarga es su verdad.
5 Ba za ka ji tsoron razanar dare, ko kibiyoyi da suke firiya da rana ba,
No temerás el terror nocturno, Ni a flecha que vuele de día,
6 ko bala’in da yake aukowa cikin duhu, ko annobar da take hallakarwa da tsakar rana.
Ni a pestilencia que ande en [la] oscuridad, Ni a mortandad que a mediodía destruya.
7 Dubu za su iya fāɗuwa a gefenka, dubu goma a hannun damanka, amma ba abin da zai zo kusa da kai.
Caerán a tu lado 1.000, Y 10.000 a tu mano derecha, Pero a ti no llegará.
8 Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.
Ciertamente mirarás con tus ojos, Y verás la recompensa de los perversos.
9 In ka mai da Mafi Ɗaukaka wurin zamanka, har ma Ubangiji wanda yake mafakata,
Por cuanto pusiste a Yavé, mi Refugio, A ʼElyón como tu Lugar de morada,
10 to, babu wani mugun abin da zai same ka, ba masifar da za tă zo kusa da tentinka.
No te vendrá mal, Ni alguna plaga tocará tu morada.
11 Gama zai umarci mala’ikunsa game da kai don su tsare ka a dukan hanyoyinka;
Pues a sus ángeles mandará con respecto a Ti, Que te guarden en todos tus caminos.
12 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.
En sus manos te llevarán Para que tu pie no tropiece en piedra.
13 Za ka taka zaki da gamsheƙa; za ka tattake babban zaki da maciji.
Sobre el león y el áspid pisarás. Pisotearás al cachorro de león y al dragón.
14 Ubangiji ya ce, “Domin ya ƙaunace ni, zan kuɓutar da shi; zan kiyaye shi, gama ya yarda da sunana.
Me amó, Por tanto Yo lo libraré. Lo pondré en alto, Porque conoció mi Nombre.
15 Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
Me invocará Y Yo le responderé. Estaré con él en la angustia. Lo libraré y lo glorificaré.
16 Da tsawon rai zan ƙosar da shi in kuma nuna masa cetona.”
Lo saciaré de larga vida y le mostraré mi salvación.