< Zabura 91 >

1 Shi wanda yake zama a wurin Mafi Ɗaukaka zai huta a cikin inuwar Maɗaukaki.
Orang yang berlindung pada Yang Mahatinggi, dan tinggal dalam naungan Yang Mahakuasa,
2 Zan ce game da Ubangiji, “Shi ne mafakata da kagarata, Allahna, wanda nake dogara.”
boleh berkata kepada TUHAN, "Engkaulah pembela dan pelindungku, Allahku, pada-Mulah aku percaya."
3 Tabbatacce zai cece ka daga tarkon mai farauta da kuma daga cututtuka masu kisa.
Ia akan melepaskan engkau dari bahaya tersembunyi, dan dari penyakit yang membawa maut.
4 Zai rufe ka da fikafikansa, a ƙarƙashin fikafikansa kuwa za ka sami mafaka; amincinsa zai zama maka garkuwa da katanga.
Ia akan menudungi engkau dengan sayap-Nya, sehingga engkau aman dalam naungan-Nya; kesetiaan-Nya seperti perisai yang melindungi engkau.
5 Ba za ka ji tsoron razanar dare, ko kibiyoyi da suke firiya da rana ba,
Engkau tak usah takut akan bahaya di waktu malam, atau serangan mendadak di waktu siang;
6 ko bala’in da yake aukowa cikin duhu, ko annobar da take hallakarwa da tsakar rana.
akan bencana yang datang di waktu gelap, atau kehancuran yang menimpa di tengah hari.
7 Dubu za su iya fāɗuwa a gefenka, dubu goma a hannun damanka, amma ba abin da zai zo kusa da kai.
Biar seribu orang tewas di sisimu, dan sepuluh ribu di sebelah kananmu, tetapi engkau sendiri tak akan cedera.
8 Za ka dai gan da idanunka yadda ake hukunta mugaye.
Bila engkau memandang di sekelilingmu, engkau melihat orang jahat kena pembalasan.
9 In ka mai da Mafi Ɗaukaka wurin zamanka, har ma Ubangiji wanda yake mafakata,
Sebab engkau menjadikan TUHAN pembelamu, Yang Mahatinggi kaujadikan pelindungmu.
10 to, babu wani mugun abin da zai same ka, ba masifar da za tă zo kusa da tentinka.
Maka engkau tak akan kena bencana, rumahmu tak akan kena ditimpa malapetaka.
11 Gama zai umarci mala’ikunsa game da kai don su tsare ka a dukan hanyoyinka;
Allah menyuruh malaikat-Nya menjagai engkau, untuk melindungi engkau ke mana saja engkau pergi.
12 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.
Mereka akan mengangkat engkau di telapak tangannya, supaya kakimu jangan tersandung pada batu.
13 Za ka taka zaki da gamsheƙa; za ka tattake babban zaki da maciji.
Engkau akan melangkahi ular dan singa, menginjak singa muda dan ular berbisa.
14 Ubangiji ya ce, “Domin ya ƙaunace ni, zan kuɓutar da shi; zan kiyaye shi, gama ya yarda da sunana.
Kata TUHAN, "Orang yang mencintai Aku akan Kuselamatkan, yang mengakui Aku akan Kulindungi.
15 Zai kira bisa sunana, zan kuma amsa masa; zan kasance tare da shi a lokacin wahala, zan kuɓutar da shi in kuma girmama shi.
Kalau ia berseru kepada-Ku, Aku akan menjawabnya. Di waktu kesesakan, Aku akan menolong dia; dia akan Kuluputkan dan Kuberi kehormatan.
16 Da tsawon rai zan ƙosar da shi in kuma nuna masa cetona.”
Dia akan Kupuaskan dengan umur panjang, dan Kuselamatkan."

< Zabura 91 >