< Zabura 90 >

1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
Tanrı adamı Musa'nın duası Ya Rab, barınak oldun bize Kuşaklar boyunca.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Dağlar var olmadan, Daha evreni ve dünyayı yaratmadan, Öncesizlikten sonsuzluğa dek Tanrı sensin.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
İnsanı toprağa döndürürsün, “Ey insanoğulları, toprağa dönün!” diyerek.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
Çünkü senin gözünde bin yıl Geçmiş bir gün, dün gibi, Bir gece nöbeti gibidir.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
İnsanları bir düş gibi siler, süpürürsün, Sabah biten ot misali:
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
Sabah filizlenir, büyür, Akşam solar, kurur.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
Eriyip bitiyoruz senin öfkenden, Kızgınlığından dehşete düşüyoruz.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Suçlarımızı önüne, Gizli günahlarımızı yüzünün ışığına çıkardın.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
Gazabından kısalıyor günlerimiz, Bir soluk gibi tükeniyor yıllarımız.
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
Ömrümüz yetmiş yıl sürüyor, Bilemedin seksen, o da sağlıklıysak; En güzel yıllar da zahmetle, kederle geçiyor, Çabucak bitiyor, uçup gidiyoruz.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Kim bilir gazabının gücünü? Çünkü öfken sana duyulan korku kadar güçlüdür.
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
Bu yüzden günlerimizi saymayı bize öğret ki, Bilgelik kazanalım.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Vazgeç, ya RAB! Öfken ne zamana dek sürecek? Acı kullarına!
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
Sabah bizi sevginle doyur, Ömrümüz boyunca sevinçle haykıralım.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Kaç gün bizi sıkıntıya soktunsa, Kaç yıl çile çektirdinse, O kadar sevindir bizi.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Yaptıkların kullarına, Görkemin onların çocuklarına görünsün.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
Tanrımız Rab bizden hoşnut kalsın. Ellerimizin emeğini boşa çıkarma. Evet, ellerimizin emeğini boşa çıkarma.

< Zabura 90 >