< Zabura 90 >

1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
Maombi ya Mose, mtu wa Mungu. Bwana, wewe umekuwa makao yetu katika vizazi vyote.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Kabla ya kuzaliwa milima au hujaumba dunia na ulimwengu, wewe ni Mungu tangu milele hata milele.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Huwarudisha watu mavumbini, ukisema, “Rudini mavumbini, enyi wanadamu.”
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
Kwa maana kwako miaka elfu ni kama siku moja iliyokwisha pita, au kama kesha la usiku.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
Unawatowesha wanadamu katika usingizi wa kifo, nao ni kama majani machanga ya asubuhi:
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
ingawa asubuhi yanachipua, ifikapo jioni huwa yamenyauka na kukauka.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
Tumeangamizwa kwa hasira yako na tumetishwa kwa ghadhabu yako.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Umeyaweka maovu yetu mbele yako, dhambi zetu za siri katika nuru ya uwepo wako.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
Tumeishi siku zetu zote chini ya ghadhabu yako, tunamaliza miaka yetu kwa kuomboleza.
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
Siku zetu za kuishi ni miaka sabini, au miaka themanini ikiwa tuna nguvu, lakini yote ni ya shida na taabu, nazo zapita haraka, nasi twatoweka.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Ni nani ajuaye nguvu za hasira yako? Kwa maana ghadhabu yako ni kubwa kama hofu tunayopaswa kuwa nayo kwako.
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
Tufundishe kuzihesabu siku zetu vizuri, ili tujipatie moyo wa hekima.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Ee Bwana, uwe na huruma! Utakawia hata lini? Wahurumie watumishi wako.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
Tushibishe asubuhi kwa upendo wako usiokoma, ili tuweze kuimba kwa shangwe na kufurahi siku zetu zote.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Utufurahishe kulingana na siku ulizotuadhibu, kulingana na miaka tuliyotaabika.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Matendo yako na yaonekane kwa watumishi wako, utukufu wako kwa watoto wao.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
Wema wa Bwana Mungu wetu uwe juu yetu; uzithibitishe kazi za mikono yetu: naam, uzithibitishe kazi za mikono yetu.

< Zabura 90 >