< Zabura 90 >

1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
Oración de Moisés varón de Dios. SEÑOR, tú nos has sido refugio en generación y en generación.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Antes que naciesen los montes, y formases la tierra y el mundo, y desde el siglo y hasta el siglo, tú eres Dios.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Vuelves al hombre hasta ser quebrantado, y dices: Convertíos, hijos de los hombres.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
Porque mil años delante de tus ojos, son como el día de ayer, que pasó, y como una de las vigilias de la noche.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
Háceslos pasar como avenida de aguas; son como sueño; como la hierba que crece en la mañana:
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
En la mañana florece y crece; á la tarde es cortada, y se seca.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
Porque con tu furor somos consumidos, y con tu ira somos conturbados.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Pusiste nuestras maldades delante de ti, nuestros yerros á la luz de tu rostro.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
Porque todos nuestros días declinan á causa de tu ira; acabamos nuestros años como un pensamiento.
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
Los días de nuestra edad son setenta años; que si en los más robustos son ochenta años, con todo su fortaleza es molestia y trabajo; porque es cortado presto, y volamos.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
¿Quién conoce la fortaleza de tu ira, y tu indignación según que debes ser temido?
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
Enséñanos de tal modo á contar nuestros días, que traigamos al corazón sabiduría.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Vuélvete, oh Jehová: ¿hasta cuándo? y aplácate para con tus siervos.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
Sácianos presto de tu misericordia: y cantaremos y nos alegraremos todos nuestros días.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Alégranos conforme á los días que nos afligiste, y los años que vimos mal.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Aparezca en tus siervos tu obra, y tu gloria sobre sus hijos.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
Y sea la luz de Jehová nuestro Dios sobre nosotros: y ordena en nosotros la obra de nuestras manos, la obra de nuestras manos confirma.

< Zabura 90 >