< Zabura 90 >
1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
Oh ʼAdonay, Tú fuiste nuestro Refugio en todas las generaciones.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Antes que nacieran las montañas, O formaras la tierra y el mundo, Desde la eternidad y hasta la eternidad, Tú eres ʼEL.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Devuelves el hombre al polvo, Y dices: Conviértanse, hijos de hombres.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
Porque 1.000 años delante de tus ojos son como el día de ayer que pasó, O como una de las vigilias de la noche.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
Los arrastras con torrentes de agua. Son como un sueño. Son como la hierba que crece en la mañana.
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
En la mañana reverdece y florece, Hacia la llegada de la noche se marchita y se seca.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
Porque somos consumidos con tu ira, Y con tu furor somos turbados.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Colocaste nuestras iniquidades ante Ti, Nuestras cosas ocultas a la luz de tu rostro.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
Porque todos nuestros días declinan a causa de tu ira. Terminamos nuestros años como un suspiro.
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
Los días de nuestra vida son 70 años, Y en los robustos, 80 años. Sin embargo, su fortaleza es molestia y trabajo, Porque pronto pasan y volamos.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
¿Quién entiende el poder de tu ira Y tu indignación como debes ser temido?
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
Enséñanos a contar nuestros días De tal modo que traigamos al corazón sabiduría.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Vuélvete, oh Yavé. ¿Hasta cuándo? Ten compasión de tus esclavos.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
En la mañana sácianos de tu misericordia, Y cantaremos y nos alegraremos todos nuestros días.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Alégranos según los días que nos afligiste, Y los años en los cuales vimos el mal.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Que tu obra aparezca en tus esclavos, Y tu majestad en sus hijos.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
Sea la gracia de ʼAdonay nuestro ʼElohim sobre nosotros, Y nos confirme la obra de nuestras manos. ¡Sí, confirma la obra de nuestras manos!