< Zabura 90 >

1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
Oratio Moysi, hominis Dei. [Domine, refugium factus es nobis a generatione in generationem.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Priusquam montes fierent, aut formaretur terra et orbis, a sæculo et usque in sæculum tu es, Deus.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Ne avertas hominem in humilitatem: et dixisti: Convertimini, filii hominum.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
Quoniam mille anni ante oculos tuos tamquam dies hesterna quæ præteriit: et custodia in nocte
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
quæ pro nihilo habentur, eorum anni erunt.
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
Mane sicut herba transeat; mane floreat, et transeat; vespere decidat, induret, et arescat.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
Quia defecimus in ira tua, et in furore tuo turbati sumus.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Posuisti iniquitates nostras in conspectu tuo; sæculum nostrum in illuminatione vultus tui.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
Quoniam omnes dies nostri defecerunt, et in ira tua defecimus. Anni nostri sicut aranea meditabuntur;
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
dies annorum nostrorum in ipsis septuaginta anni. Si autem in potentatibus octoginta anni, et amplius eorum labor et dolor; quoniam supervenit mansuetudo, et corripiemur.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Quis novit potestatem iræ tuæ, et præ timore tuo iram tuam
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
dinumerare? Dexteram tuam sic notam fac, et eruditos corde in sapientia.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Convertere, Domine; usquequo? et deprecabilis esto super servos tuos.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
Repleti sumus mane misericordia tua; et exsultavimus, et delectati sumus omnibus diebus nostris.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Lætati sumus pro diebus quibus nos humiliasti; annis quibus vidimus mala.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Respice in servos tuos et in opera tua, et dirige filios eorum.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
Et sit splendor Domini Dei nostri super nos, et opera manuum nostrarum dirige super nos, et opus manuum nostrarum dirige.]

< Zabura 90 >