< Zabura 90 >

1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
A Prayer of Moses, the man of God. Lord, a habitation Thou — Thou hast been, To us — in generation and generation,
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Before mountains were brought forth, And Thou dost form the earth and the world, Even from age unto age Thou [art] God.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Thou turnest man unto a bruised thing, And sayest, Turn back, ye sons of men.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
For a thousand years in Thine eyes [are] as yesterday, For it passeth on, yea, a watch by night.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
Thou hast inundated them, they are asleep, In the morning as grass he changeth.
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
In the morning it flourisheth, and hath changed, At evening it is cut down, and hath withered.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
For we were consumed in Thine anger, And in Thy fury we have been troubled.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Thou hast set our iniquities before Thee, Our hidden things at the light of Thy face,
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
For all our days pined away in Thy wrath, We consumed our years as a (meditation)
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
Days of our years, in them [are] seventy years, And if, by reason of might, eighty years, Yet [is] their enlargement labour and vanity, For it hath been cut off hastily, and we fly away.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Who knoweth the power of Thine anger? And according to Thy fear — Thy wrath?
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
To number our days aright let [us] know, And we bring the heart to wisdom.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Turn back, O Jehovah, till when? And repent concerning Thy servants.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
Satisfy us at morn [with] Thy kindness, And we sing and rejoice all our days.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Cause us to rejoice according to the days Wherein Thou hast afflicted us, The years we have seen evil.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Let Thy work appear unto Thy servants, And Thine honour on their sons.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
And let the pleasantness of Jehovah our God be upon us, And the work of our hands establish on us, Yea, the work of our hands establish it!

< Zabura 90 >