< Zabura 90 >
1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
The preier of Moises, the man of God. Lord, thou art maad help to vs; fro generacioun in to generacioun.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Bifore that hillis weren maad, ether the erthe and the world was formed; fro the world and in to the world thou art God.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Turne thou not awei a man in to lownesse; and thou seidist, Ye sones of men, be conuertid.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
For a thousynde yeer ben bifore thin iyen; as yistirdai, which is passid, and as keping in the niyt.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
The yeeris of hem schulen be; that ben had for nouyt.
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
Eerli passe he, as an eerbe, eerli florische he, and passe; in the euentid falle he doun, be he hard, and wexe drie.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
For we han failid in thin ire; and we ben disturblid in thi strong veniaunce.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
Thou hast set oure wickidnessis in thi siyt; oure world in the liytning of thi cheer.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
For alle oure daies han failid; and we han failid in thin ire. Oure yeris schulen bithenke, as an yreyn;
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
the daies of oure yeeris ben in tho seuenti yeeris. Forsothe, if fourescoor yeer ben in myyti men; and the more tyme of hem is trauel and sorewe. For myldenesse cam aboue; and we schulen be chastisid.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Who knew the power of thin ire; and durste noumbre thin ire for thi drede?
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
Make thi riythond so knowun; and make men lerned in herte bi wisdom.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Lord, be thou conuertid sumdeel; and be thou able to be preied on thi seruauntis.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
We weren fillid eerli with thi merci; we maden ful out ioye, and we delitiden in alle oure daies.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
We weren glad for the daies in whiche thou madist vs meke; for the yeeris in whiche we siyen yuels.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Lord, biholde thou into thi seruauntis, and in to thi werkis; and dresse thou the sones of hem.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
And the schynyng of oure Lord God be on vs; and dresse thou the werkis of oure hondis on vs, and dresse thou the werk of oure hondis.