< Zabura 90 >
1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
A PRAYER OF MOSES, THE MAN OF GOD. Lord, You have been a habitation, To us—in generation and generation,
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Before mountains were brought forth, And You form the earth and the world, Even from age to age You [are] God.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
You turn man to a bruised thing, And say, Return, you sons of men.
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
For one thousand years in Your eyes [are] as yesterday, For it passes on, indeed, [as] a watch by night.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
You have inundated them, they are asleep, In the morning he changes as grass.
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
In the morning it flourishes, and has changed, At evening it is cut down, and has withered.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
For we were consumed in Your anger, And we have been troubled in Your fury.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
You have set our iniquities before You, Our hidden things at the light of Your face,
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
For all our days pined away in Your wrath, We consumed our years as a (meditation)
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
The days of our years, in them [are] seventy years, And if, by reason of might, eighty years, Yet their enlargement [is] labor and vanity, For it has been cut off quickly, and we fly away.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Who knows the power of Your anger? And according to Your fear—Your wrath?
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
Let [us] know to number our days correctly, And we bring the heart to wisdom.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Turn back, O YHWH, until when? And regret concerning Your servants.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
Satisfy us at morning [with] Your kindness, And we sing and rejoice all our days.
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
Cause us to rejoice according to the days Wherein You have afflicted us, The years we have seen evil.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
Let Your work appear to Your servants, And Your honor on their sons.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
And let the pleasantness of our God YHWH be on us, And establish on us the work of our hands, Indeed, establish the work of our hands!