< Zabura 90 >
1 Addu’ar Musa Mutumin Allah. Ubangiji kai ne mazauninmu cikin dukan zamanai.
A Prayer of Moses the man of God. Lord, you have been our refuge in all generations.
2 Kafin a haifi duwatsu ko a fid da ƙasa da duniya, daga madawwami zuwa madawwami kai Allah ne.
Before the mountains existed, and [before] the earth and the world were formed, even from age to age, You are.
3 Ka komar da mutane zuwa ƙura, kana cewa, “Ku koma ƙura, ya ku’ya’yan mutane.”
Turn not man back to [his] low place, whereas you said, Return, you sons of men?
4 Gama shekaru dubu a gabanka kamar kwana ɗaya ne da ya wuce, ko sa’a guda na dare.
For a thousand years in your sight are as the yesterday which is past, and as a watch in the night.
5 Ka share mutane cikin barcin mutuwa; suna kama da sabuwa ciyawar safiya,
Years shall be vanity to them: let the morning pass away as grass.
6 ko da yake da safe takan yi sabuwar huda da yamma sai ta bushe ta kuma yanƙwane.
In the morning let it flower, and pass away: in the evening let it droop, let it be withered and dried up.
7 An cinye mu ta wurin fushinka mun kuma razana ta wurin hasalarka.
For we have perished in your anger, and in your wrath we have been troubled.
8 Ka ajiye laifinmu a gabanka, asirin zunubanmu a hasken kasancewarka.
You have set our transgressions before you: our age is in the light of your countenance.
9 Dukan kwanakinmu sun wuce ƙarƙashin fushinka; mun gama shekarunmu da nishi.
For all our days are gone, and we have passed away in your wrath: our years have spun out their tale as a spider.
10 Tsawon kwanakinmu shekaru saba’in ne, ko tamanin, in muna da ƙarfi; duk da haka tsawonsu wahaloli ne kawai da ɓacin rai, gama da sauri suke wucewa, ta mu kuma ta ƙare.
[As for] the days of our years, in them are seventy years; and if [men should be] in strength, eighty years: and the greater part of them would be labour and trouble; for weakness overtakes us, and we shall be chastened.
11 Wa ya san ƙarfin fushinka? Gama hasalarka tana da girma kamar tsoron da ya dace da kai.
Who knows the power of your wrath?
12 Ka koya mana yawan kwanakinmu daidai, don mu sami zuciyar hikima.
and [who knows how] to number [his days] because of the fear of your wrath? So manifest your right hand, and those that are instructed in wisdom in the heart.
13 Ka ji mu, ya Ubangiji! Har yaushe zai ci gaba? Ka ji tausayin bayinka.
Return, O Lord, how long? and be entreated concerning your servants.
14 Ka ƙosar da mu da safe da ƙaunarka marar ƙarewa, don mu rera don yabo, mu kuma yi murna dukan kwanakinmu.
We have been satisfied in the morning with your mercy; and we did exult and rejoice:
15 Faranta mana zuciya kamar yawan kwanakin da muka sha azaba, kamar yawan shekarun da muka ga wahala.
let us rejoice in all our days, in return for the days wherein you did afflict us, the years wherein we saw evil.
16 Bari a nuna ayyukanka ga bayinka, darajarka ga’ya’yansu.
And look upon your servants, and upon your works; and guide their children.
17 Bari alherin shugabanmu Allah yă kasance a kanmu; ka albarkaci mana aikin hannuwanmu, I, ka albarkaci aikin hannuwanmu.
And let the brightness of the Lord our God be upon us: and do you direct for us the works of our hands.