< Zabura 9 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
I MEN kapina leowa jan nan monion i meler, o kajokajoiia duen japwilim omui dodok kapuriamui kan karoj.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I men pereperen o polauleki komui o kauleki mar omui; komui me lapalapia,
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
Pwe re kotin kaloedier ai imwintiti kan, irail pupedier o melar.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
Pwe re kotin apwali ia ni ai pun o ai dodok. Komui kainpokedi pon mol omui duen jaunkapun pun amen.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Kom kotin kapun on men liki kan o kotin kamela me japun kan, kom kotin kawelar mar arail kokolata.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
Imwintiti o joredier, a namenokalar melel. Komui kotin wuketedi kanim akan; o jolar, me pan taman irail ada o tou ar akan.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
A Ieowa pan kotin kaunda kokolata. A kotin kaonopada mol a, pwen kadeikada.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
O a pan kotin kadeikada jappa ni pun, o kakaunda wei kan pun.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
Ieowa jile pan me jamama kan, jilepa ni anjau apwal.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
I me irail, me aja mar omui kin liki komui, pwe komui jota kin muei jan irail, me kin rapaki komui, Main Ieowa.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Kauleki Ieowa, me kin kaunda nan Jion. Komail padaki on wei kan a wiawia!
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
Pwe a kotin taman irail ada o kotin kainoma nta’rail. A jota kin kotin maliela likwir en me jamama kan.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Main Ieowa, kom kotin maki on ia. Re kotin mani ai apwal ren ai imwintiti kan, kom kotin dore ia la jan nan wanim en mela.
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
Pwe i en kajokajoiia duen omui dodok kapuriamui pan wanim en nain Jion, perenki jauaj pa om.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
Men liki kan pupedi on nan por o, me pein irail weiradar, o nil’rail lodi on injar, me pein irail wiadar.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
I me kitail ajaki, Ieowa me kotin kapun pun. Me japun kan jalidi on pein ar dodok en pa ar akan. (Jela)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
Me japun kan en lokidokila nan wajan mela, o men liki kan karoj, me kin monokela Kot. (Sheol )
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
Pwe me jamama o jota pan monokinokla kokolata, o me luet akan jota pan kaporoporeki mal kokolata.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Main, kom kotida! Pwe aramaj ender pwaida, a men liki kan karoj en pakadeikada mo omui.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Main, kotiki on ir men kamajak, pwe men liki kan en dedeki, me re udan aramaj eta. (Jela)