< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
برای رهبر سرایندگان: مزمور داوود، در مایۀ «مرگ پسر». ای خداوند، با تمام وجود تو را می‌ستایم و از کارهای شگفت‌انگیز تو سخن می‌رانم.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
تو شادی و خوشی من هستی و من در وصف تو، ای خدای متعال، می‌سرایم.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
دشمنانم عقب‌نشینی کرده، در حضور تو بر زمین خواهند افتاد و هلاک خواهند شد،
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
زیرا تو ای داور عادل بر مسند خود نشسته‌ای و از حق من دفاع می‌کنی.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
تو قومهای شرور را محکوم و نابود کرده‌ای و نام آنها را از صفحهٔ روزگار محو ساخته‌ای.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
دشمنان ما را به کلی ریشه‌کن نموده‌ای و شهرهای آنها را ویران کرده‌ای به طوری که حتی نامی از آنها نیز باقی نمانده است.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
خداوند تا به ابد پادشاه است. او مسند داوری خود را برقرار کرده
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
تا بر قومهای دنیا با عدل و انصاف داوری نماید.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
خداوند پناهگاه رنجدیدگان است و ایشان را در سختیها حفظ می‌کند.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
خداوندا، کسانی که تو را می‌شناسند، به تو پناه می‌آورند زیرا تو هرگز طالبان خود را ترک نکرده‌ای.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
در وصف خداوند که در اورشلیم سلطنت می‌کند، بسرایید! کارهای او را در میان همهٔ قومها اعلام کنید!
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
زیرا او قاتلان را بی‌سزا نخواهد گذاشت و فریاد ستمدیدگان را فراموش نخواهد کرد.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
ای خداوند، ببین دشمنانم چگونه به من ظلم می‌کنند. بر من رحم کن و مرا از چنگال مرگ رهایی دِه
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
تا تو را در حضور همهٔ مردم اورشلیم ستایش کنم و به سبب این رهایی شادی نمایم.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
دشمنان در چاهی که برای دیگران کنده بودند، افتاده‌اند و در دامهایی که برای دیگران گذاشته بودند گرفتار شده‌اند.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
خداوند بدکاران را در دامهای خودشان گرفتار می‌کند و نشان می‌دهد که خدای عادلی است.
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
همهٔ بدکاران و تمام قومهایی که خدا را از یاد می‌برند هلاک خواهند شد. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
بیچارگان و ستمدیدگان سرانجام به یاد آورده خواهند شد و امیدشان بر باد نخواهد رفت.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
برخیز، ای خداوند! نگذار انسان پیروز شود؛ باشد که قومها در حضور تو داوری شوند.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
آنها را به وحشت انداز تا بفهمند که انسان فانی‌ای بیش نیستند.

< Zabura 9 >