< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
למנצח עלמות לבן מזמור לדוד אודה יהוה בכל לבי אספרה כל נפלאותיך׃
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
אשמחה ואעלצה בך אזמרה שמך עליון׃
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
בשוב אויבי אחור יכשלו ויאבדו מפניך׃
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
כי עשית משפטי ודיני ישבת לכסא שופט צדק׃
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
גערת גוים אבדת רשע שמם מחית לעולם ועד׃
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
האויב תמו חרבות לנצח וערים נתשת אבד זכרם המה׃
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
ויהוה לעולם ישב כונן למשפט כסאו׃
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
והוא ישפט תבל בצדק ידין לאמים במישרים׃
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
ויהי יהוה משגב לדך משגב לעתות בצרה׃
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
ויבטחו בך יודעי שמך כי לא עזבת דרשיך יהוה׃
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
זמרו ליהוה ישב ציון הגידו בעמים עלילותיו׃
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
כי דרש דמים אותם זכר לא שכח צעקת עניים׃
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
חננני יהוה ראה עניי משנאי מרוממי משערי מות׃
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
למען אספרה כל תהלתיך בשערי בת ציון אגילה בישועתך׃
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
טבעו גוים בשחת עשו ברשת זו טמנו נלכדה רגלם׃
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
נודע יהוה משפט עשה בפעל כפיו נוקש רשע הגיון סלה׃
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
ישובו רשעים לשאולה כל גוים שכחי אלהים׃ (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
כי לא לנצח ישכח אביון תקות ענוים תאבד לעד׃
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
קומה יהוה אל יעז אנוש ישפטו גוים על פניך׃
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
שיתה יהוה מורה להם ידעו גוים אנוש המה סלה׃

< Zabura 9 >