< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
Pour la fin, pour les mystères du Fils, psaume de David. Je vous louerai, Seigneur, en tout mon cœur; je raconterai toutes vos merveilles.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
Je me réjouirai et je tressaillirai d’allégresse en vous; je chanterai votre nom, ô Très-Haut.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
Quand vous aurez mis mon ennemi en fuite, ils seront sans force, et ils périront devant votre face.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
Puisque vous m’avez fait justice et pris en main ma cause: vous vous êtes assis sur votre trône, vous qui jugez selon la justice.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Vous avez gourmande les nations, et l’impie a péri; vous avez effacé leur nom pour l’éternité, et pour les siècles des siècles.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
Les armes de l’ennemi ont perdu leur force pour toujours, et vous avez détruit leurs villes. Leur mémoire a péri avec bruit:
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
Et le Seigneur demeure éternellement. Il a préparé son trône pour le jugement:
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
Et lui-même jugera le globe de la terre avec équité, il jugera les peuples avec justice.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
Et le Seigneur s’est fait le refuge du pauvre, son aide au temps du besoin, dans la tribulation.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Qu’ils espèrent donc en vous ceux qui connaissent votre nom, puisque vous n’avez pas délaissé ceux qui vous cherchent. Seigneur.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Chantez le Seigneur, qui habite dans Sion; annoncez ses desseins parmi les nations.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
Puisqu’il s’est souvenu d’eux, en demandant compte du sang, et qu’il n’a pas oublié le cri du pauvre.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Ayez pitié de moi. Seigneur, voyez l’abaissement où m’ont réduit mes ennemis.
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
Vous qui me relevez des portes de la mort, afin que je publie toutes vos louanges aux portes de la fille de Sion.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
Je tressaillirai de joie dans votre salut. Les nations ont été englouties dans le gouffre qu’elles avaient préparé; Leur pied a été pris dans le même lacet qu’elles avaient caché.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
Ainsi on reconnaîtra que le Seigneur rend justice; le pécheur a été pris dans les œuvres de ses mains.
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
Que de même les pécheurs soient précipités dans l’enfer, et toutes les nations qui oublient Dieu. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
Car le pauvre ne sera pas pour toujours en oubli; la patience des pauvres ne sera pas toujours vaine.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Levez-vous, Seigneur, que l’homme ne se fortifie point: que les nations soient jugées en votre présence.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Établissez, Seigneur, un législateur sur eux, afin que les peuples sachent qu’ils ne sont que des hommes.

< Zabura 9 >