< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
Je célébrerai l'Éternel de tout mon cœur; je raconterai toutes tes merveilles.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
Je m'égaierai, je me réjouirai en toi, je chanterai ton nom, ô Dieu Très-Haut!
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
Parce que mes ennemis reculent en arrière, qu'ils tombent et périssent devant ta face.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
Car tu m'as fait droit, tu as défendu ma cause; tu t'es assis sur ton trône en juste juge.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Tu as châtié les nations, tu as fait périr le méchant, tu as effacé leur nom pour toujours, à perpétuité.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
C'en est fait des ennemis; plus que des ruines! Tu as détruit leurs villes et leur mémoire a péri.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
Mais l'Éternel règne à jamais; il prépare son trône pour le jugement.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
Il jugera le monde avec justice; il jugera les peuples avec équité.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
L'Éternel sera le refuge de l'opprimé, son refuge au temps de la détresse.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Et ceux qui connaissent ton nom, se confieront en toi; car tu n'abandonnes pas ceux qui te cherchent, ô Éternel!
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Chantez à l'Éternel qui habite en Sion; annoncez parmi les peuples ses hauts faits!
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
Car il venge le sang versé, et il s'en souvient; il n'oublie point le cri des affligés.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Aie pitié de moi, ô Éternel! Vois l'affliction que m'ont causée mes ennemis, toi qui me fais remonter des portes de la mort!
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
Afin que je publie toutes tes louanges dans les portes de la fille de Sion, et que je me réjouisse de ton salut.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
Les nations sont tombées dans la fosse qu'elles avaient faite; leur pied s'est pris au filet qu'elles avaient caché.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
L'Éternel s'est fait connaître, il a exercé le jugement; le méchant s'est enlacé dans l'ouvrage de ses mains. (Higgajon, Sélah, Jeu d'instruments, Pause)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
Les méchants reculeront jusqu'aux enfers, et toutes les nations qui oublient Dieu. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
Car le pauvre ne sera pas oublié pour toujours; et l'attente des affligés ne périra pas à perpétuité!
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Lève-toi, Éternel! Que l'homme ne prévale point, que les peuples soient jugés devant ta face!
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Éternel, répands sur eux la terreur; que les peuples sachent qu'ils ne sont que des hommes! (Sélah)

< Zabura 9 >