< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
Au maître de chant. Sur l'air " Mort au fils ". Psaume de David. Je louerai Yahweh de tout mon cœur, je raconterai toutes tes merveilles.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
Je me réjouirai et je tressaillerai en toi, je chanterai ton nom, ô Très-Haut.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
Mes ennemis reculent, ils trébuchent et tombent devant ta face.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
Car tu as fait triompher mon droit et ma cause, tu t'es assis sur ton trône en juste juge.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Tu as châtié les nations, tu as fait périr l'impie, tu as effacé leur nom pour toujours et à jamais.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
L'ennemi est anéanti! Des ruines pour toujours! Des villes que tu as renversées! Leur souvenir a disparu!
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
Mais Yahweh siège à jamais, il a dressé son trône pour le jugement.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
Il juge le monde avec justice, il juge les peuples avec droiture.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
Et Yahweh est un refuge pour l'opprimé, un refuge au temps de la détresse.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
En toi se confient tous ceux qui connaissent ton nom; car tu ne délaisses pas ceux qui te cherchent, Yahweh.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Chantez à Yahweh, qui réside en Sion, publiez parmi les peuples ses hauts faits.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
Car celui qui redemande le sang versé s'en est souvenu, il n'a point oublié le cri des affligés.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
" Aie pitié de moi, Yahweh, disaient-ils; vois l'affliction où m'ont réduit mes ennemis, toi qui me retires des portes de la mort,
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
afin que je puisse raconter toutes les louanges, aux portes de la fille de Sion, tressaillir de joie à cause de ton salut. "
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
Les nations sont tombées dans la fosse qu'elles ont creusée, dans le lacet qu'elles ont caché s'est pris leur pied.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
Yahweh s'est montré, il a exercé le jugement, dans l'œuvre de ses mains il a enlacé l'impie. (Higgaion) Séla.
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
Les impies retournent au schéol, toutes les nations qui oublient Dieu. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
Car le malheureux n'est pas toujours oublié, l'espérance des affligés ne périt pas à jamais.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Lève-toi, Yahweh! Que l'homme ne triomphe pas! Que les nations soient jugées devant ta face!
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Répands sur elles l'épouvante, Yahweh; que les peuples sachent qu'ils sont des hommes! — Séla.

< Zabura 9 >