< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
To the chief Musician upon Muthlabben, A Psalm of David. I will praise thee, O LORD, with my whole heart; I will show forth all thy marvellous works.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will be glad and rejoice in thee: I will sing praise to thy name, O thou most High.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemies are turned back, they shall fall and perish at thy presence.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For thou hast maintained my right and my cause; thou satest on the throne judging right.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Thou hast rebuked the heathen, thou hast destroyed the wicked, thou hast put out their name for ever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
O thou enemy, destructions are come to a perpetual end: and thou hast destroyed cities; their memorial hath perished with them.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
But the LORD shall endure for ever: he hath prepared his throne for judgment.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
And he shall judge the world in righteousness, he shall minister judgment to the people in uprightness.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
The LORD also will be a refuge for the oppressed, a refuge in times of trouble.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
And they that know thy name will put their trust in thee: for thou, LORD, hast not forsaken them that seek thee.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing praises to the LORD, who dwelleth in Zion: declare among the people his doings.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
When he maketh inquisition for blood, he remembereth them: he forgetteth not the cry of the humble.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Have mercy upon me, O LORD; consider my trouble which I suffer from them that hate me, thou that liftest me up from the gates of death:
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
That I may show forth all thy praise in the gates of the daughter of Zion: I will rejoice in thy salvation.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
The heathen are sunk down in the pit that they made: in the net which they hid is their own foot taken.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
The LORD is known by the judgment which he executeth: the wicked is snared in the work of his own hands. (Higgaion, Selah)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
The wicked shall be turned into hell, and all the nations that forget God. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For the needy shall not always be forgotten: the expectation of the poor shall not perish for ever.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Arise, O LORD; let not man prevail: let the heathen be judged in thy sight.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Put them in fear, O LORD: that the nations may know themselves to be but men. (Selah)

< Zabura 9 >