< Zabura 9 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
For the chief musician; set to Muth Labben style. A psalm of David. I will give thanks to Yahweh with my whole heart; I will tell about all your marvelous deeds.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will be glad and rejoice in you; I will sing praise to your name, Most High!
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemies turn back, they stumble and perish before you.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For you have defended my just cause; you sit on your throne, a righteous judge!
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
You rebuked the nations; you have destroyed the wicked; you have blotted out their name forever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
The enemy crumbled like ruins when you overthrew their cities. All remembrance of them has perished.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
But Yahweh remains forever; he has established his throne for justice.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
He will judge the world with righteousness, and he will execute judgment for the nations with fairness.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
Yahweh also will be a stronghold for the oppressed, a stronghold in times of trouble.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Those who know your name trust in you, for you, Yahweh, do not abandon those who seek you.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing praises to Yahweh, who rules in Zion; tell the nations what he has done.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
For the God who avenges bloodshed remembers; he does not forget the cry of the oppressed.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Have mercy on me, Yahweh; see how I am oppressed by those who hate me, you who can snatch me from the gates of death.
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
Oh, that I might proclaim all your praise. In the gates of the daughter of Zion I will rejoice in your salvation!
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
The nations have sunk down into the pit that they made; their feet are caught in the net that they hid.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
Yahweh has made himself known; he has executed judgment; the wicked is ensnared by his own actions. (Selah)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
The wicked are turned back and sent to Sheol, all the nations that forget God. (Sheol )
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For the needy will not always be forgotten, nor will the hope of the oppressed be forever dashed.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Arise, Yahweh; do not let man win against you; may the nations be judged in your sight.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Terrify them, Yahweh; may the nations know that they are mere men. (Selah)