< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
Unto the end, for the hidden things of the Son. A psalm for David. I will give praise to thee, O Lord, with my whole heart: I will relate all thy wonders.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will be glad and rejoice in thee: I will sing to thy name, O thou most high.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemy shall be turned back: they shall be weakened and perish before thy face.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For thou hast maintained my judgment and my cause: thou hast sat on the throne, who judgest justice.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Thou hast rebuked the Gentiles, and the wicked one hath perished: thou hast blotted out their name for ever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
The swords of the enemy have failed unto the end: and their cities thou hast destroyed. Their memory hath perished with a noise.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
But the Lord remaineth for ever. He hath prepared his throne in judgment:
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
And he shall judge the world in equity, he shall judge the people in justice.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
And the Lord is become a refuge for the poor: a helper in due time in tribulation.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
And let them trust in thee who know thy name: for thou hast not forsaken them that seek thee, O Lord.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing ye to the Lord, who dwelleth in Sion: declare his ways among the Gentiles:
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
For requiring their blood he hath remembered the: he hath not forgotten the cry of the poor.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Have mercy on me, O Lord: see my humiliation which I suffer from my enemies.
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
Thou that liftest me up from the gates of death, that I may declare all thy praises in the gates of the daughter of Sion.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
I will rejoice in thy salvation: the Gentiles have stuck fast in the destruction which they have prepared. Their foot hath been taken in the very snare which they hid.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
The Lord shall be known when he executeth judgments: the sinner hath been caught in the works of his own hands.
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
The wicked shall be turned into hell, all the nations that forget God. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For the poor man shall not be forgotten to the end: the patience of the poor shall not perish for ever.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Arise, O Lord, let not man be strengthened: let the Gentiles be judged in thy sight.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Appoint, O Lord, a lawgiver over them: that the Gentiles may know themselves to be but men.

< Zabura 9 >