< Zabura 9 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
For the choirmaster. To the tune of “The Death of the Son.” A Psalm of David. I will give thanks to the LORD with all my heart; I will recount all Your wonders.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will be glad and rejoice in You; I will sing praise to Your name, O Most High.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemies retreat, they stumble and perish before You.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For You have upheld my just cause; You sit on Your throne judging righteously.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
You have rebuked the nations; You have destroyed the wicked; You have erased their name forever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
The enemy has come to eternal ruin, and You have uprooted their cities; the very memory of them has vanished.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
But the LORD abides forever; He has established His throne for judgment.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
He judges the world with justice; He governs the people with equity.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
The LORD is a refuge for the oppressed, a stronghold in times of trouble.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
Those who know Your name trust in You, for You, O LORD, have not forsaken those who seek You.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing praises to the LORD, who dwells in Zion; proclaim His deeds among the nations.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
For the Avenger of bloodshed remembers; He does not ignore the cry of the afflicted.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Be merciful to me, O LORD; see how my enemies afflict me! Lift me up from the gates of death,
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
that I may declare all Your praises— that within the gates of Daughter Zion I may rejoice in Your salvation.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
The nations have fallen into a pit of their making; their feet are caught in the net they have hidden.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
The LORD is known by the justice He brings; the wicked are ensnared by the work of their hands.
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
The wicked will return to Sheol— all the nations who forget God. (Sheol )
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For the needy will not always be forgotten; nor the hope of the oppressed forever dashed.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Rise up, O LORD, do not let man prevail; let the nations be judged in Your presence.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Lay terror upon them, O LORD; let the nations know they are but men.