< Zabura 9 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
I will give thanks to Jehovah with my whole heart. I will show forth all thy marvelous works.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will be glad and exult in thee. I will sing praise to thy name, O thou Most High.
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemies turn back, they stumble and perish at thy presence.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For thou have maintained my right and my cause. Thou sit in the throne judging righteously.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Thou have rebuked the nations. Thou have destroyed the wicked. Thou have blotted out their name forever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
The enemy have come to an end. They are desolate forever, and the cities which thou have overthrown. The very memory of them is perished,
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
but Jehovah will endure forever. He has prepared his throne for judgment,
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
and he will judge the world in righteousness. He will minister justice to the peoples in uprightness.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
Jehovah will also be a high tower for the oppressed, a high tower in times of trouble.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
And those who know thy name will put their trust in thee, for thou, Jehovah, have not forsaken those who seek thee.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing praises to Jehovah, who dwells in Zion. Declare among the people his doings.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
For he who makes inquiry for blood remembers them. He does not forget the cry of the poor.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Have mercy upon me, O Jehovah. Behold my affliction from those who hate me, thou who lifts me up from the gates of death
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
that I may show forth all thy praise. In the gates of the daughter of Zion I will rejoice in thy salvation.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
The nations are sunk down in the pit that they made. In the net which they hid, their own foot is taken.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
Jehovah has made himself known. He has executed justice. The wicked man is snared in the work of his own hands. (Higgaion, Selah)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
Wicked men shall be turned back to Sheol, even all the nations that forget God. (Sheol )
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For a needy man shall not always be forgotten, nor the expectation of the poor perish forever.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Arise, O Jehovah, let not man prevail. Let the nations be judged in thy sight.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Put them in fear, O Jehovah. Let the nations know themselves to be but men. (Selah)