< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Un salmo (masquil) de Ethan el Ezraite Cantaré del gran amor del Señor para siempre; le contaré a todas las generaciones de tu fidelidad.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Porque he dicho, “Tu amor que nunca falla durará para siempre; tu fidelidad durará tanto como los cielos”.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
Tú dijiste, “He llegado a un acuerdo con mi elegido, le di una promesa de unión a mi siervo David:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
Me aseguraré que tu linaje perdure por siempre; mantendré tu trono seguro a través de todas las generaciones”. (Selah)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Señor, todos los seres celestiales cantarán de las maravillosas cosas que has hecho; los ángeles se unirán para cantar de tu fidelidad.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Porque, ¿Quién en el cielo se puede comparar al Señor? ¿Quién es como el Señor incluso entre los ángeles?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
La asamblea celestial teme a Dios; todos los que lo rodean son abrumados por su presencia.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Señor, Dios todo poderoso, ¿Quién es tan poderoso como tú? En todo esto, Señor, tú eres digno de confianza.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Tú gobiernas sobre los mares embravecidos; tú calmas sus olas tormentosas.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Aplastaste a Rahab (el mostruo marino) hasta la muerte; dispersaste a tus enemigos con tu poder.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Los cielos te pertenecen, y la tierra también; tú hiciste el mundo, y todo lo que en él está.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Creaste el norte y el sur; el Monte Tabor y el Monte Hermón te celebran.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Tu brazo es poderoso. Tu mano es fuerte. Tu diestra se mantiene en alto al mando.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Tu carácter de bondad y equidad son la base de tu gobierno; el amor y la confianza están siempre contigo.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Cuán felices son aquellos que saben cómo gritar tus alabanzas, Señor. Porque ellos viven en la luz de tu presencia.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Te celebran de día y de noche, se alegran tanto de que hagas lo que es correcto.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Ellos confían a ti su gloria y sus fuerzas; levántanos por tu poder.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Sí, el Señor es el único que nos protege, y nuestro rey pertenece al santo de Israel.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Una vez hablaste en una visión a tu siervo fiel y dijiste: “Le he dado fuerza al guerrero que he escogido de entre el pueblo para convertirlo en rey.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
He escogido a David, mi siervo, y lo he ungido con el aceite de mi santidad.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
He puesto mi mano sobre él para reafirmarlo; y lo he hecho fuerte con mi brazo poderoso.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Sus enemigos no lo destruirán; los malvados no lo harán caer al suelo.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Acabaré con sus enemigos antes que él; derribaré a aquellos que lo odian.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
La fidelidad de mi amor estarán con él, y con mi ayuda saldrá victorioso.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Extenderé su gobierno desde el Mar Mediterráneo hasta el río Éufrates
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Él invocará mi nombre, diciendo, ‘Tú eres mi padre, mi Dios, y la roca de mi salvación’.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Lo haré también mi primogénito, el más grande de los reyes de la tierra.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Lo amaré por siempre; mi pacto con él nunca llegará a un fin.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Me aseguraré de que su linaje real dure para siempre; su dinastía continuará, y será tan extensa como los cielos.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Pero si sus descendientes abandonan mi ley, si no siguen mis reglas,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
si rompen mis decretos, y no siguen mis mandamientos,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
castigaré su rebelión golpeándolos con una vara, y su pecados los herirán con un látigo.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Sin embargo, no alejaré mi amor de él; no romperé la promesa que le he hecho.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
No anularé el acuerdo que tengo con él; no alteraré una sola palabra de lo que he dicho.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
He hecho un voto a David por mi carácter santo, prometiendo de que no le mentiría.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Su linaje real permanecerá para siempre, y su dinastía permanecerá ante mí tanto como el sol ha permanecido.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Continuará como la luna, un testigo de los cielos que ha perdurado desde siempre”. (Selah)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
¡Pero tú me has rechazado y me has abandonado! ¡Estás enojado con tu rey escogido!
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
¡Has roto el acuerdo que tenías con él; has tirado su corona al suelo!
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Has derribado sus muros de defensa; has arruinado su fortaleza.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Todo el que ha pasado por allí lo ha robado; se ha convertido en objeto de burla para las naciones cercanas.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Has hecho a sus enemigos fuertes; has permitido que celebren su victoria.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Has rechazado su espada afilada; no lo has ayudado en combate.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Retiraste su gloria; lanzaste su trono al suelo.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Lo has hecho envejecer antes de tiempo; lo has humillado totalmente. (Selah)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
¿Por cuánto tiempo más, Señor? ¿Te esconderás de nosotros para siempre? ¿Dejarás a tu ira arder como fuego?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Recuérdame, ¡mi vida es muy corta! ¿Por qué te molestaste en crear una humanidad inútil?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
No hay nadie que no muera, nadie puede salvarse a sí mismo del poder de la tumba. (Selah) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
¿Donde está, oh Señor, el gran amor que solías tener? El que le prometiste lealmente a David
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
¡No olvides, Señor! ¡Cómo están siendo humillados tus siervos! ¡Estoy agobiado con los insultos de tantas naciones!
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
Tus enemigos se burlan de mí, Señor, se mofan de tu rey a dondequiera que va.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Que el señor sea bendito por siempre. Amén y amén.

< Zabura 89 >