< Zabura 89 >
1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
O Gospodovih milostih bom prepeval na veke, s svojimi usti bom vsem rodovom razglašal tvojo zvestobo.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Kajti rekel sem: »Usmiljenje bo zgrajeno na veke, svojo zvestobo boš utrdil v samih nebesih.«
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
S svojim izbranim sem sklenil zavezo, prisegel sem Davidu, svojemu služabniku:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
»Tvoje seme bom utrdil na veke in tvoj prestol zgradil za vse rodove.« (Sela)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Nebesa bodo hvalila tvoje čudeže, oh Gospod, tudi tvojo zvestobo v skupnosti svetih.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Kajti kdo na nebu bi bil lahko primerjan z Gospodom? Kdo izmed sinov mogočnega bi bil lahko podoben Gospodu?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Boga se je silno bati v zboru svetih in spoštujejo ga vsi tisti, ki so okoli njega.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Oh Gospod Bog nad bojevniki, kdo je močan Gospod, podoben tebi ali tvoji zvestobi naokoli tebe?
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Ti vladaš besnenju morja; ko njegovi valovi vstanejo, jih ti umirjaš.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Zlomil si Rahaba na koščke, kakor nekoga, ki je umorjen, s svojim močnim laktom si razkropil svoje sovražnike.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Nebo je tvoje, tudi zemlja je tvoja; kar se tiče zemeljskega [kroga] in njegove polnosti, si jih ti utemeljil.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Sever in jug, ti si ju ustvaril; Tabor in Hermon se bosta veselila v tvojem imenu.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Ti imaš mogočen laket, močna je tvoja roka in visoka je tvoja desnica.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Pravičnost in sodba sta prebivališče tvojega prestola, usmiljenje in resnica bosta šla pred tvojim obličjem.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Blagoslovljeno je ljudstvo, ki pozna radosten zvok. Hodili bodo, oh Gospod, v svetlobi tvojega obličja.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
V tvojem imenu se bodo veselili ves dan in v tvoji pravičnosti bodo povišani.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Kajti ti si slava njihove moči in v tvoji naklonjenosti bo naš rog povišan.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Kajti Gospod je naša obramba in Sveti Izraelov je naš kralj.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Potem svojemu svetemu spregovoriš v videnju in rečeš: »Položil sem pomoč na nekoga, ki je mogočen, povišal sem enega izbranega izmed ljudstva.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
Našel sem Davida, svojega služabnika; s svojim svetim oljem sem ga mazilil.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Z njim bo moja roka utrjena; tudi moj laket ga bo krepil.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Sovražnik se ne bo maščeval nad njim niti ga sin zlobnosti [ne bo] prizadel.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Njegove sovražnike bom premagal pred njegovim obrazom in nadlegoval tiste, ki ga sovražijo.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
Toda z njim bosta moja zvestoba in moje usmiljenje in v mojem imenu bo povišan njegov rog.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Njegovo roko bom postavil tudi na morje in njegovo desnico na reke.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Klical bo k meni: ›Ti si moj oče, moj Bog in skala rešitve moje duše.‹
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Prav tako mu bom dal svojega prvorojenca, višje kakor kralje zemlje.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Svoje usmiljenje bom zanj ohranil na vékomaj in moja zaveza bo trdno stala z njim.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Tudi njegovemu semenu bom storil, da ostane na veke in njegov prestol kakor nebeški dnevi.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Če njegovi otroci zapustijo mojo postavo in ne hodijo po mojih sodbah,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
če prelomijo moje zakone in se ne držijo mojih zapovedi,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
potem bom s palico obiskal njihov prestopek in njihovo krivičnost z bičanjem.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Vendar pa svoje ljubeče skrbnosti ne bom popolnoma odvzel od njega niti svoji zvestobi [ne bom] pustil, da se izneveri.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Svoje zaveze ne bom prelomil niti predrugačil stvari, ki je odšla iz mojih ustnic.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Enkrat sem prisegel pri svoji svetosti, da Davidu ne bom lagal.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Njegovo seme bo ostalo na veke in njegov prestol kakor sonce pred menoj.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Kakor luna bo utrjen na veke in kakor zvesta priča na nebu.« (Sela)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Toda ti si zavrgel in prezrl, ogorčen si bil s svojim maziljencem.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Razveljavil si zavezo svojega služabnika. Njegovo krono si oskrunil in jo vrgel na tla.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Porušil si vse njegove ograje; njegova oporišča si privedel do propada.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Vsi mimoidoči ga plenijo. Graja je svojim sosedom.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Dvignil si desnico njegovih nasprotnikov; vsem njegovim sovražnikom si storil, da se veselijo.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Obrnil si tudi ostrino njegovega meča in ga nisi naredil, da se zoperstavi v bitki.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Njegovi slavi si storil, da preneha in njegov prestol si vrgel na tla.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Dneve njegove mladosti si skrajšal. Pokril si ga s sramoto. (Sela)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Doklej, Gospod? Se hočeš skrivati na veke? Bo tvoj bes gorel kakor ogenj?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Spomni se, kako kratek je moj čas. Zakaj si vse ljudi naredil zaman?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
Kateri človek je, kdor živi in ne bo videl smrti? Ali bo svojo dušo osvobodil pred roko groba? (Sela) (Sheol )
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Gospod, kje so tvoje prejšnje ljubeče skrbnosti, katere v svoji resnici prisegaš Davidu?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Spomni se, Gospod, graje svojih služabnikov; kako v svojih prsih nosim grajo vseh mogočnih ljudi,
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
s čimer so grajali tvoji sovražniki, oh Gospod, s čimer so grajali stopinje tvojega maziljenca.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Blagoslovljen bodi Gospod na vékomaj. Amen in Amen.