< Zabura 89 >
1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Milosti æu Gospodnje pjevati uvijek, od koljena na koljeno javljaæu istinu tvoju ustima svojima.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Jer znam da je zavavijek osnovana milost, i na nebesima da si utvrdio istinu svoju, rekavši:
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
“Uèinih zavjet s izbranim svojim, zakleh se Davidu, sluzi svojemu:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
Dovijeka æu utvrðivati sjeme tvoje i prijesto tvoj ureðivati od koljena do koljena.
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Nebo kazuje èudesa tvoja, Gospode, i istinu tvoju sabor svetijeh.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Jer ko je nad oblacima ravan Gospodu? ko æe se izjednaèiti s Gospodom meðu sinovima Božijim?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Bogu se valja klanjati na saboru svetijeh, strašniji je od svijeh koji su oko njega.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Gospode, Bože nad vojskama! ko je silan kao ti, Bože? I istina je tvoja oko tebe.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Ti vladaš nad silom morskom; kad podigne vale svoje, ti ih ukroæavaš.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Ti si oborio oholi Misir kao ranjenika, krjepkom mišicom svojom rasijao si neprijatelje svoje.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Tvoje je nebo i tvoja je zemlja; ti si sazdao vasiljenu i što je god u njoj.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Sjever i jug ti si stvorio, Tavor i Ermon o tvom se imenu raduje.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Tvoja je mišica krjepka, silna je ruka tvoja, i visoka desnica tvoja.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Blagost je i pravda podnožje prijestolu tvojemu, milost i istina ide pred licem tvojim.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Blago narodu koji zna trubnu pokliè! Gospode! u svjetlosti lica tvojega oni hode;
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Imenom se tvojim raduju vas dan, i pravdom tvojom uzvišuju se.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Jer si ti krasota sile njihove, i po milosti tvojoj uzvišuje se rog naš.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Jer je od Gospoda obrana naša, i od svetoga Izrailjeva car naš.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Tada si govorio u utvari vjernima svojim, i rekao: “poslah pomoæ junaku, uzvisih izbranoga svojega iz naroda.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
Naðoh Davida slugu svojega, svetim uljem svojim pomazah ga.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Ruka æe moja biti jednako s njim, i mišica moja krijepiæe ga.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Neæe ga neprijatelj nadvladati, i sin bezakonja neæe mu dosaditi.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Potræu pred licem njegovijem neprijatelje njegove, i nenavidnike njegove poraziæu.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
Istina je moja i milost moja s njim; i u moje ime uzvisiæe se rog njegov.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Pružiæu na more ruku njegovu, i na rijeke desnicu njegovu.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
On æe me zvati: ti si otac moj, Bog moj i grad spasenja mojega.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
I ja æu ga uèiniti prvencem, višim od careva zemaljskih.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Dovijeka æu mu hraniti milost svoju, i zavjet je moj s njim vjeran.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Produljiæu sjeme njegovo dovijeka, i prijesto njegov kao dane nebeske.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Ako sinovi njegovi ostave zakon moj, i ne uzidu u zapovijestima mojim;
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
Ako pogaze uredbe moje, i zapovijesti mojih ne saèuvaju,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
Onda æu ih pokarati prutom za nepokornost, i ranama za bezakonje njihovo;
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Ali milosti svoje neæu uzeti od njega, niti æu prevrnuti istinom svojom;
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Neæu pogaziti zavjeta svojega, i što je izašlo iz usta mojih neæu poreæi.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Jednom se zakleh svetošæu svojom; zar da slažem Davidu?
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Sjeme æe njegovo trajati dovijeka, i prijesto njegov kao sunce preda mnom;
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
On æe stajati uvijek kao mjesec i vjerni svjedok u oblacima.”
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
A sad si odbacio i zanemario, razgnjevio si se na pomazanika svojega;
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Zanemario si zavjet sa slugom svojim, bacio si na zemlju vijenac njegov.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Razvalio si sve ograde njegove, gradove njegove obratio si u zidine.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Plijene ga svi koji prolaze onuda, posta potsmijeh u susjeda svojijeh.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Uzvisio si desnicu neprijatelja njegovijeh, obradovao si sve protivnike njegove.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Zavratio si ostrice maèa njegova, i nijesi ga ukrijepio u boju;
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Uzeo si mu svjetlost, i prijesto njegov oborio si na zemlju;
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Skratio si dane mladosti njegove i obukao ga u sramotu.
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Dokle æeš se, Gospode, jednako odvraæati, dokle æe kao oganj plamtjeti gnjev tvoj?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Opomeni se kakav je vijek moj, kako si ni na što stvorio sve sinove Adamove?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
Koji je èovjek živio i nije smrti vidio, i izbavio dušu svoju iz ruku paklenijeh? (Sheol )
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Gdje su preðašnje milosti tvoje, Gospode? Kleo si se Davidu istinom svojom.
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Opomeni se, Gospode, prijekora sluga svojih, koji nosim u njedrima svojim od svijeh silnijeh naroda,
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
Kojim kore neprijatelji tvoji, Gospode, kojim kore trag pomazanika tvojega.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Blagosloven Gospod uvijek! Amin, amin.