< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Instrução de Etã Ezraíta: Cantarei das bondades do SENHOR para sempre; de geração em geração com minha boca anunciarei tua fidelidade.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Porque eu disse: [Tua] bondade durará para sempre; confirmaste tua fidelidade até nos céus.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
[Tu disseste]: Eu fiz um pacto com o meu escolhido, jurei a meu servo Davi. [Eu lhe disse]:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
Confirmarei tua semente para sempre, e farei teu trono continuar de geração em geração. (Selá)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Que os céus louvem as tuas maravilhas, SENHOR; pois tua fidelidade [está] na congregação dos santos.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Porque quem no céu pode se comparar ao SENHOR? E quem é semelhante ao SENHOR entre os filhos dos poderosos?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Deus é terrível na assembleia dos santos, e mais temível do que todos os que estão ao seu redor.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Ó SENHOR Deus dos exércitos, quem é poderoso como tu, SENHOR? E tua fidelidade está ao redor de ti.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Tu dominas a arrogância do mar; quando suas ondas se levantam, tu as aquietas.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Quebraste a Raabe como que ferida de morte; com teu braço forte espalhaste os teus inimigos.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Teus são os céus, também tua é a terra; o mundo e sua plenitude, tu os fundaste.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
O norte e o sul, tu os criaste; Tabor e Hermon têm muita alegria em teu nome.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Tu tens um braço poderoso; forte é tua mão, [e] alta está tua mão direita.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Justiça e juízo são a base de teu trono; bondade e verdade vão adiante de teu rosto.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Bem-aventurado é o povo que entende o grito de alegria; ó SENHOR, eles andarão na luz de tua face.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Em teu nome se alegrarão o dia todo, e em tua justiça serão exaltados.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Porque tu és a glória de sua força, e por tua boa vontade nosso poder é exaltado.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Porque ao SENHOR pertence nosso escudo; e o Santo de Israel é nosso Rei.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Então em visão falaste ao teu santo, e disseste: Pus o socorro sobre um valente; exaltei a um escolhido dentre o povo.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
Achei a Davi, meu servo; eu o ungi com meu óleo santo.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Com ele minha mão será firme; e também meu braço o fortalecerá.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
O inimigo não tomará suas riquezas, nem o filho da perversidade o afligirá.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Porém eu espancarei seus adversários, e ferirei aos que o odeiam.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
E minha fidelidade e minha bondade serão com ele; e em meu nome seu poder será exaltado.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Porei a mão dele no mar, e sua mão direita nos rios.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Ele me chamará: Tu és meu Pai, meu Deus, e a rocha da minha salvação.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Eu também o porei como primogênito, mais alto que todos os reis da terra.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Manterei minha bondade para com ele para sempre, e meu pacto com ele será firme.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Conservarei sua semente para sempre, e o trono dele como os dias dos céus.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Se seus filhos deixarem minha Lei, e não andarem em meus juízos,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
Se profanarem os meus estatutos, e não guardarem os meus mandamentos,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
Então punirei a transgressão deles com vara, e a perversidade deles com açoite,
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Porém nunca tirarei minha bondade dele, nem falharei em minha fidelidade.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Não quebrarei o meu pacto, e o que saiu dos meus lábios não mudarei.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Uma vez jurei por minha Santidade, [e] nunca mentirei a Davi.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
A semente dele durará para sempre, e o trono dele [será] como o sol perante mim.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Assim como a lua, ele será confirmado para sempre; e a testemunha no céu é fiel. (Selá)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Porém tu te rebelaste, e [o] rejeitaste; ficaste irado contra o teu Ungido.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Anulaste o pacto do teu servo; desonraste a coroa dele [lançando-a] contra a terra.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Derrubaste todos os seus muros; quebraste suas fortificações.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Todos os que passam pelo caminho o despojaram; ele foi humilhado por seus vizinhos.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Levantaste a mão direita de seus adversários; alegraste a todos os inimigos dele.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Também deixaste de afiar sua espada; e não o sustentaste na batalha.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Fizeste cessar sua formosura; e derrubaste seu trono à terra.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Encurtaste os dias de sua cidade; cobriste-o de vergonha. (Selá)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Até quando, SENHOR? Tu te esconderás para sempre? Arderá teu furor como o fogo?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Lembra-te de que curta é minha vida; por que criarias em vão todos os filhos dos homens?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
Que homem vive, que não experimente a morte? Livrará ele a sua alma do poder do Xeol? (Selá) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Senhor, onde estão as tuas bondades do passado, que juraste a Davi por tua fidelidade?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Lembra-te, Senhor, da humilhação de teus servos, que eu trago em meu peito, [causada] por todos e grandes povos.
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
Com [humilhação] os teus inimigos insultam, SENHOR, com a qual insultam os passos do teu ungido.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Bendito [seja] o SENHOR para todo o sempre. Amém, e Amém.

< Zabura 89 >