< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Nyanyian pengajaran Etan, orang Ezrahi.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Sebab aku tahu kasih-Mu kekal abadi, kesetiaan-Mu teguh seperti langit.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
Engkau berkata, "Aku sudah membuat perjanjian dengan orang pilihan-Ku; Aku telah bersumpah kepada Daud, hamba-Ku:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
'Takhtamu Kupertahankan untuk selama-lamanya, turun-temurun anak cucumu akan mendudukinya.'"
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Sidang surgawi memuji perbuatan-perbuatan-Mu yang ajaib, dan menyanyikan kesetiaan-Mu, TUHAN.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Di langit tak ada yang seperti Engkau, ya TUHAN, tak ada makhluk surgawi yang menyamai Engkau.
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Engkau dihormati di kalangan para suci, ditakuti lebih dari semua di sekeliling-Mu.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
TUHAN, Allah Yang Mahakuasa, siapakah sekuat Engkau? Engkau setia dalam segala-galanya ya TUHAN.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Engkau menguasai laut yang bergelora, dan meredakan ombaknya yang dahsyat.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Rahab, naga laut, Kauremukkan dan Kaubunuh, dengan tangan kuat Kaukalahkan musuh-musuh-Mu.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Langit dan bumi adalah milik-Mu, dunia dan segala isinya ciptaan-Mu.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Engkaulah yang menjadikan utara dan selatan, Gunung Tabor dan Hermon bersorak-sorai bagi-Mu.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Betapa besar kuasa-Mu, dan betapa hebat kekuatan-Mu!
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Keadilan dan hukum adalah dasar kerajaan-Mu, kasih dan kesetiaan nyata dalam segala tindakan-Mu.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Berbahagialah bangsa yang beribadat dengan gembira, yang hidup dalam cahaya kehadiran-Mu, TUHAN.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Sepanjang hari mereka bersukacita dan tetap teguh, karena kebaikan-Mu.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Engkau memberi kami kemenangan yang gilang-gemilang, karena kebaikan-Mulah kami menang.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Sebab pelindung kami adalah orang pilihan-Mu, ya TUHAN; raja kami adalah milik Allah Kudus Israel.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Dahulu kala dalam suatu penglihatan, Engkau berkata kepada hamba-Mu yang setia, "Aku telah menolong seorang pahlawan, seorang yang Kupilih dari rakyat telah Kutinggikan.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
Aku telah menemukan Daud, hamba-Ku, dan Kulantik dia dengan minyak upacara.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Kekuatan-Ku akan selalu melindunginya, kuasa-Ku akan menguatkan dia.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Ia tak akan dikalahkan musuh, dan tak akan ditindas orang jahat.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Semua musuhnya akan Kubinasakan, Kubunuh siapa saja yang membenci dia.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
Aku akan tetap mengasihi dia dan setia kepadanya, dan membuat dia semakin berkuasa.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Kerajaannya akan Kuluaskan, dari Laut Tengah sampai ke Sungai Efrat.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Ia akan berkata kepada-Ku, 'Engkaulah Bapaku, Allahku, pelindung dan penyelamatku.'
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Aku akan menjadikan dia putra-Ku yang sulung, yang paling agung di antara semua raja.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Dia akan tetap Kukasihi sampai kekal, perjanjian-Ku dengan dia tetap teguh.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Takhtanya Kupertahankan selama langit ada di atas bumi, turun-temurun anak cucunya akan mendudukinya.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Tetapi kalau keturunannya melanggar hukum-Ku, dan tidak hidup menurut perintah-Ku,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
kalau mereka tidak mengindahkan ketetapan-Ku dan mengabaikan peraturan-Ku,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
mereka Kuhukum dengan cambuk karena pelanggarannya, dan Kutimpa dengan bencana karena dosa-dosanya.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Tetapi Aku akan tetap mengasihi Daud, dan tak akan mengingkari kesetiaan-Ku.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Perjanjian-Ku dengan dia takkan Kubatalkan, dari janji-Ku tak satu pun Kutarik kembali.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Sekali untuk selamanya Aku bersumpah demi nama-Ku yang suci; Aku tak akan berbohong kepada Daud.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Takhtanya akan bertahan selama matahari ada, turun-temurun anak cucunya akan mendudukinya.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Kerajaannya tetap ada seperti bulan, saksi setia di awan-awan."
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Tetapi sekarang Engkau marah kepada raja, Engkau membuang dan menolak orang pilihan-Mu.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Kaubatalkan perjanjian-Mu dengan hamba-Mu, mahkotanya Kaulemparkan ke dalam lumpur.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Kaurobohkan tembok-tembok kotanya, benteng-benteng Kaujadikan reruntuhan.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Semua orang yang lewat merampas miliknya, ia menjadi bahan ejekan bagi tetangganya.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Engkau memberi kemenangan kepada musuh-musuhnya, dan membuat semua lawannya bergembira.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Bahkan senjatanya Kaujadikan tak berguna, Engkau tidak menolong dia dalam perang.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Kauakhiri kuasanya yang semarak, takhtanya Kaucampakkan ke tanah.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Engkau memperpendek masa mudanya, dan menutupi dia dengan malu.
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Sampai kapan Engkau bersembunyi, ya TUHAN? Sampai kapan kemarahan-Mu berkobar seperti api?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Ingatlah aku betapa singkatnya hidupku ini, Kauciptakan manusia sebagai makhluk yang fana.
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
Siapakah yang dapat hidup terus dan tidak mati? Siapakah yang dapat luput dari kuburan? (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Ya TUHAN, di manakah tanda kasih-Mu yang semula, yang Kaujanjikan kepada Daud demi kesetiaan-Mu?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Ingatlah ya TUHAN, bagaimana hamba-Mu ini dicela, aku menanggung penghinaan banyak bangsa.
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
Musuh-musuh-Mu menghina raja pilihan-Mu, ya TUHAN, mengejek dia ke mana saja ia pergi.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Pujilah TUHAN untuk selama-lamanya. Jadilah demikian! Amin!

< Zabura 89 >