< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Intelligence d’Ethan l’Ezrahite. Je chanterai éternellement les miséricordes du Seigneur.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Parce que vous avez dit: Éternellement la miséricorde sera fondée dans les cieux; votre vérité y sera affermie.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
J’ai établi une alliance avec mes élus; j’ai juré à David mon serviteur:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
J’affermirai ta race, en sorte qu’elle dure éternellement, Et je fonderai ton trône pour toutes les générations.
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Les cieux publieront vos merveilles, Seigneur, comme aussi votre vérité? dans l’assemblée des saints.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Car qui, dans les nues, sera égal au Seigneur; et qui sera semblable à Dieu parmi les fils de Dieu?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Le Dieu qui est glorifié dans l’assemblée des saints, il est grand et terrible au-dessus de tous ceux qui sont autour de lui.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Seigneur, Dieu des armées, qui est semblable à vous; vous êtes puissant. Seigneur, et la vérité est autour de vous.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
C’est vous qui dominez sur la puissance de la mer, et le mouvement de ses flots, c’est vous qui l’apaisez.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
C’est vous qui avez humilié un superbe, comme un blessé mortellement: par la force de votre bras vous avez dispersé vos ennemis.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
À vous sont les cieux, et à vous est la terre: le globe de la terre et sa plénitude, c’est vous qui les avez fondés;
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
L’aquilon et la mer, c’est vous qui les avez créés.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Votre bras est puissant.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
La justice et le jugement sont la base de votre trône. La miséricorde et la vérité précéderont votre face;
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Bienheureux le peuple qui sait se réjouir en vous. Seigneur, c’est à la lumière de votre visage qu’ils marcheront,
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Et en votre nom qu’ils tressailliront de joie tout le jour, et c’est par votre justice qu’ils seront exaltés.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Puisque la gloire de leur puissance, c’est vous; et que par votre bienveillance notre corne sera exaltée.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Parce que c’est le Seigneur qui nous a pris sous sa protection, et le saint d’Israël, notre roi.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Alors vous parlâtes dans une vision à vos saints et vous dites: J’ai mis mon secours dans un homme puissant; et j’ai exalté un élu du milieu de mon peuple.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
J’ai trouvé David mon serviteur, je l’ai oint de mon huile sainte.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Car ma main le secourra, et mon bras le fortifiera.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Un ennemi ne pourra rien contre lui, et un fils d’iniquité ne pourra plus lui nuire.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Et je taillerai en pièces à sa face ses ennemis, et ceux qui le haïssent, je les mettrai en fuite.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
Et ma vérité et ma miséricorde seront avec lui, et en mon nom sera exaltée sa corne.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Et je poserai sa main sur la mer, et sa droite sur les fleuves.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Lui-même m’invoquera, disant: C’est vous qui êtes mon père, mon Dieu, et le garant de mon salut;
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Et moi, je l’établirai mon premier-né, et plus élevé que tous les rois de la terre.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Éternellement je lui conserverai ma miséricorde, et mon alliance lui sera fidèle.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Et j’établirai sa race dans les siècles des siècles, et son trône comme les jours du ciel.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Mais si ses fils abandonnent ma loi, s’ils ne marchent pas dans mes jugements,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
S’ils profanent mes justes ordonnances, et ne gardent point mes commandements,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
Je visiterai avec une verge leurs iniquités, et avec des fléaux leurs péchés.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Mais je ne retirerai pas ma miséricorde de lui, et je ne manquerai pas à ma vérité;
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Et je ne profanerai point mon alliance, et les paroles qui sortent de ma bouche, je ne les rendrai pas vaines.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
J’ai juré une fois par ma sainteté, que je ne mentirai pas à David:
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Sa race demeurera éternellement.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Et son trône sera comme le soleil en ma présence, et comme la pleine lune, éternellement, et comme le témoin fidèle dans le ciel.
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Et vous cependant, vous avez rejeté et méprisé: vous avez éloigné votre Christ.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Vous avez renversé l’alliance faite avec votre serviteur; vous avez profané sur la terre son sanctuaire.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Vous avez détruit toutes ses haies; vous avez répandu dans ses forteresses la frayeur.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Tous ceux qui passaient dans le chemin l’ont pillé: il est devenu l’opprobre de ses voisins.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Vous avez exalté la droite de ceux qui l’opprimaient; vous avez réjoui tous ses ennemis.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Vous avez détourné l’aide de son glaive, et vous ne l’avez pas secouru dans la guère.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Vous l’avez dépouillé de son éclat, et son trône, vous l’avez brisé contre la terre.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Vous abrégez les jours de sa durée: vous l’avez couvert d’ignominie.
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Jusques à quand. Seigneur, détournerez-vous entièrement votre face? Jusques à quand s’embrasera votre colère comme un feu?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Souvenez-vous de ce qu’est mon être: car est-ce en vain que vous avez créé tous les fils des hommes?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
Quel est l’homme qui vivra, et qui ne verra pas la mort? qui retirera son âme de la main de l’enfer? (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Où sont vos miséricordes anciennes, Seigneur, telles que vous les avez jurées à David dans votre vérité?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Souvenez-vous, Seigneur, de l’opprobre (que j’ai gardé dans mon sein), que vos serviteurs ont souffert de la part d’un grand nombre de nations;
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
Souvenez-vous de ce que vos ennemis ont reproché, Seigneur, de ce qu’ils ont reproché le changement de votre Christ.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Béni le Seigneur éternellement! ainsi soit, ainsi soit.

< Zabura 89 >