< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Instruction d’Éthan, l’Ezrakhite. Je chanterai à toujours les bontés de l’Éternel; de génération en génération je ferai connaître de ma bouche ta fidélité.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Car j’ai dit: La bonté sera édifiée pour toujours; dans les cieux mêmes tu établiras ta fidélité.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
J’ai fait alliance avec mon élu, j’ai juré à David, mon serviteur:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
J’établirai ta semence pour toujours, et j’édifierai ton trône de génération en génération. (Sélah)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Et les cieux célébreront tes merveilles, ô Éternel! oui, ta fidélité, dans la congrégation des saints.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Car qui, dans les nues, peut être comparé à l’Éternel? Qui, parmi les fils des forts, est semblable à l’Éternel?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Dieu est extrêmement redoutable dans l’assemblée des saints, et terrible au milieu de tous ceux qui l’entourent.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Éternel, Dieu des armées, qui est comme toi, puissant Jah? Et ta fidélité est tout autour de toi.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Toi, tu domines l’orgueil de la mer; quand ses flots se soulèvent, toi tu les apaises.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Toi, tu as abattu Rahab comme un homme tué; par le bras de ta force tu as dispersé tes ennemis.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
À toi les cieux, et à toi la terre; le monde et tout ce qu’il contient, toi tu l’as fondé.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Le nord et le midi, toi tu les as créés; le Thabor et l’Hermon exultent en ton nom.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
À toi est le bras de puissance; ta main est forte; ta droite est haut élevée.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
La justice et le jugement sont les bases de ton trône; la bonté et la vérité marchent devant ta face.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Bienheureux le peuple qui connaît le cri de joie! Ils marchent, ô Éternel! à la lumière de ta face.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Ils s’égaient en ton nom tout le jour, et sont haut élevés par ta justice.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Car tu es la gloire de leur force; et dans ton bon plaisir notre corne sera haut élevée.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
Car l’Éternel est notre bouclier, et le Saint d’Israël, notre roi.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Alors tu parlas en vision de ton saint, et tu dis: J’ai placé du secours sur un homme puissant, j’ai haut élevé un élu d’entre le peuple.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
J’ai trouvé David, mon serviteur; je l’ai oint de mon huile sainte;
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Ma main sera fermement avec lui, et mon bras le fortifiera;
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
L’ennemi ne le pressurera pas et le fils d’iniquité ne l’affligera pas;
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
J’abattrai ses adversaires devant sa face, et je frapperai ceux qui le haïssent;
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
Et ma fidélité et ma bonté seront avec lui, et, par mon nom, sa corne sera élevée.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
Et j’ai mis sa main à la mer, et sa droite dans les fleuves.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Lui me criera: Tu es mon père, mon Dieu, et le rocher de mon salut.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Aussi moi, je ferai de lui le premier-né, le plus élevé des rois de la terre.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Je lui garderai ma bonté à toujours, et mon alliance lui sera assurée.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Et je ferai subsister sa semence à perpétuité, et son trône comme les jours des cieux.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Si ses fils abandonnent ma loi et ne marchent pas dans mes ordonnances,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
S’ils violent mes statuts et ne gardent pas mes commandements,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
Je visiterai leur transgression avec la verge, et leur iniquité avec des coups;
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Mais je ne retirerai pas de lui ma bonté, et je ne démentirai pas ma fidélité;
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Je ne violerai point mon alliance, et je ne changerai pas ce qui est sorti de mes lèvres.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
J’ai une fois juré par ma sainteté, si [jamais] je mens à David!
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Sa semence sera à toujours, et son trône comme le soleil devant moi.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Comme la lune, il sera affermi pour toujours; et le témoin dans les nues en est ferme. (Sélah)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Mais tu l’as rejeté et tu l’as méprisé, tu as été courroucé contre ton oint.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Tu as répudié l’alliance de ton serviteur, tu as profané sa couronne jusqu’en terre;
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Tu as rompu toutes ses clôtures, tu as mis en ruine ses forteresses:
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Tous ceux qui passent le pillent; il est en opprobre à ses voisins.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Tu as élevé la droite de ses adversaires, tu as réjoui tous ses ennemis;
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Tu as retourné le tranchant de son épée, et tu ne l’as pas soutenu dans la bataille.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Tu as fait cesser son éclat, et tu as jeté par terre son trône;
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
Tu as abrégé les jours de sa jeunesse, tu l’as couvert de honte. (Sélah)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Jusques à quand, ô Éternel, te cacheras-tu à toujours, [et] ta fureur brûlera-t-elle comme un feu?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Souviens-toi, quant à moi, de ce qu’est la vie: pourquoi as-tu créé tous les fils des hommes [pour n’être que] vanité?
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
Qui est l’homme qui vit et qui ne verra pas la mort, – qui sauvera son âme de la main du shéol? (Sélah) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Où sont, Seigneur, tes premières bontés, que tu as jurées à David dans ta fidélité?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Souviens-toi, Seigneur, de l’opprobre de tes serviteurs, – je porte dans mon sein [celui de] tous les grands peuples, –
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
[L’opprobre] dont tes ennemis couvrent, ô Éternel, dont ils couvrent les pas de ton oint.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Béni soit l’Éternel pour toujours! Amen, oui, amen!

< Zabura 89 >