< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
I will sing of the loving kindness of Jehovah forever. With my mouth I will make known thy faithfulness to all generations.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
For I have said, Mercy shall be built up forever. Thy faithfulness thou will establish in the very heavens.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
I have made a covenant with my chosen. I have sworn to David my servant:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
Thy seed I will establish forever, and build up thy throne to all generations. (Selah)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
And the heavens shall praise thy wonders, O Jehovah, thy faithfulness also in the assembly of the sanctified.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
For who in the clouds can be compared to Jehovah? Who among the sons of the mighty is like Jehovah,
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
a God very awesome in the council of the holy ones, and to be feared above all those who are round about him?
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
O Jehovah God of hosts, who is a mighty one like thee, O Jehovah? And thy faithfulness is round about thee.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Thou rule the pride of the sea. When the waves of it arise, thou still them.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Thou have broken Rahab in pieces, as a wounded man. Thou have scattered thine enemies with the arm of thy strength.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
The heavens are thine, the earth also is thine, the world and the fullness of it; thou have founded them.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
The north and the south, thou have created them. Tabor and Hermon rejoice in thy name.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Thou have a mighty arm. Strong is thy hand, and high is thy right hand.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Righteousness and justice are the foundation of thy throne. Loving kindness and truth go before thy face.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Blessed is the people who know the joyful sound. They walk, O Jehovah, in the light of thy countenance.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
In thy name do they rejoice all the day, and in thy righteousness are they exalted.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
For thou are the glory of their strength, and in thy favor our horn shall be exalted.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
For our shield belongs to Jehovah, and our king to the Holy One of Israel.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Then thou spoke in a vision to thy sanctified, and said, I have laid help upon a mighty man. I have exalted a chosen man out of the people.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
I have found David my servant. With my holy oil I have anointed him,
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
with whom my hand shall be established. My arm also shall strengthen him.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
The enemy shall not exact from him, nor the son of wickedness afflict him.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
And I will beat down his adversaries before him, and smite those who hate him,
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
but my faithfulness and my loving kindness shall be with him, and in my name shall his horn be exalted.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
I will also set his hand on the sea, and his right hand on the rivers.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
He shall cry to me, Thou are my Father, my God, and the rock of my salvation.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
I also will make him firstborn, the highest of the kings of the earth.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
I will keep my loving kindness for him for evermore. And my covenant shall stand fast with him.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
I will also make his seed to endure forever, and his throne as the days of heaven.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
If his sons forsake my law, and walk not in my ordinances,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
if they break my statutes, and keep not my commandments,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
then I will visit their transgression with the rod, and their iniquity with stripes,
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
but my loving kindness I will not utterly take from him, nor allow my faithfulness to fail.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
I will not break my covenant, nor alter the thing that is gone out of my lips.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
I have sworn once by my holiness; I will not lie to David.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
His seed shall endure forever, and his throne as the sun before me.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
It shall be established forever as the moon, and as the faithful witness in the sky. (Selah)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
But thou have cast off and rejected. Thou have been angry with thine anointed.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Thou have abhorred the covenant of thy servant. Thou have profaned his crown to the ground.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Thou have broken down all his hedges. Thou have brought his strongholds to ruin.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
All who pass by the way rob him. He has become a reproach to his neighbors.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Thou have exalted the right hand of his adversaries. Thou have made all his enemies to rejoice.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
Yea, thou turn back the edge of his sword, and have not made him to stand in the battle.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
Thou have made his brightness to cease, and cast his throne down to the ground.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
The days of his youth thou have shortened. Thou have covered him with shame. (Selah)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
How long, O Jehovah? Will thou hide thyself forever? Shall thy wrath burn like fire?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
O remember how short my time is, for what vanity thou have created all the sons of men!
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
What man is he who shall live and not see death, who shall deliver his soul from the power of Sheol? (Selah) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Lord, where are thy former loving kindnesses, which thou swore to David in thy faithfulness?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Remember, Lord, the reproach of thy servants, how I bear in my bosom all the mighty peoples,
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
with which thine enemies have reproached, O Jehovah, with which they have reproached the footsteps of thine anointed.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Blessed be Jehovah for evermore. Truly, and Truly.

< Zabura 89 >