< Zabura 89 >

1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
(En Maskil af Ezraitten Etan.) Om HERRENs, Nåde vil jeg evigt synge, fra Slægt til Slægt med min Mund forkynde din Trofasthed.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Thi du har sagt: "En evig Bygning er Nåden!" I Himlen har du grundfæstet din Trofasthed.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
Jeg sluttede en Pagt med min udvalgte, tilsvor David, min Tjener:
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
"Jeg lader din Sæd bestå for evigt, jeg bygger din Trone fra Slægt til Slægt!" (Sela)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Og Himlen priser dit Under, HERRE, din Trofasthed i de Helliges Forsamling.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
Thi hvem i Sky er HERRENs Lige, hvo er som HERREN iblandt Guds Sønner?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
En forfærdelig Gud i de Helliges Kreds, stor og frygtelig over alle omkring ham.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
HERRE, Hærskarers Gud, hvo er som du? HERRE, din Nåde og Trofasthed omgiver dig.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Du mestrer Havets Overmod; når Bølgerne bruser, stiller du dem.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Du knuste Rahab som en fældet Kriger, splitted dine Fjender med vældig Arm.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Din er Himlen, og din er Jorden, du grundede Jorderig med dets Fylde.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Norden og Sønden skabte du, Tabor og Hermon jubler over dit Navn.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Du har en Arm med Vælde, din Hånd er stærk, din højre løftet.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Retfærd og Ret er din Trones Grundvold, Nåde og Sandhed står for dit Åsyn.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
Saligt det Folk, der kender til Frydesang, vandrer, HERRE, i dit Åsyns Lys!
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
De lovsynger Dagen igennem dit Navn, ophøjes ved din Retfærdighed.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Thi du er vor Styrkes Stolthed, du løfter vort Horn ved din Yndest;
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
thi vort Skjold er hos HERREN, vor Konge er Israels Hellige!
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Du taled engang i et Syn til dine fromme: "Krone satte jeg på en Helt, ophøjed en Yngling af Folket;
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
jeg har fundet David, min Tjener, salvet ham med min hellige Olie;
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
thi min Hånd skal holde ham fast, og min Arm skal give ham Styrke.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Ingen Fjende skal overvælde ham, ingen Nidding trykke ham ned;
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
jeg knuser hans Fjender foran ham og nedstøder dem, der bader ham;
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
med ham skal min Trofasthed og Miskundhed være, hans Horn skal løfte sig ved mit Navn;
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
jeg lægger Havet under hans Hånd og Strømmene under hans højre;
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
mig skal han kalde: min Fader, min Gud og min Frelses Klippe.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Jeg gør ham til førstefødt, den største blandt Jordens Konger;
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
jeg bevarer for evigt min Miskundhed mod ham, min Pagt skal holdes ham troligt;
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
jeg lader hans Æt bestå for evigt, hans Trone, så længe Himlen er til.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
Hvis hans Sønner svigter min Lov og ikke følger mine Lovbud,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
hvis de bryder min Vedtægt og ikke holder mit Bud,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
da hjemsøger jeg deres Synd med Ris, deres Brøde med hårde Slag;
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
men min Nåde tager jeg ikke fra ham, min Trofasthed svigter jeg ikke;
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
jeg bryder ikke min Pagt og ændrer ej mine Læbers Udsagn.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Ved min Hellighed svor jeg een Gang for alle - David sviger jeg ikke:
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Hans Æt skal blive for evigt, hans Trone for mig som Solen,
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
stå fast som Månen for evigt, og Vidnet på Himlen er sanddru, (Sela)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Men du har forstødt og forkastet din Salvede og handlet i Vrede imod ham;
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Pagten med din Tjener har du brudt, vanæret hans Krone og trådt den i Støvet;
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
du har nedbrudt alle hans Mure, i Grus har du lagt hans Fæstninger;
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
alle vejfarende plyndrer ham, sine Naboer blev han til Spot.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
Du har løftet hans Uvenners højre og glædet alle hans Fjender;
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
hans Sværd lod du vige for Fjenden, du holdt ham ej oppe i Kampen;
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
du vristed ham Staven af Hænde og styrted hans Trone til Jorden,
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
afkorted hans Ungdoms Dage og hylled ham ind i Skam. (Sela)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
Hvor længe vil du skjule dig, HERRE, for evigt, hvor længe skal din Vrede lue som Ild?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Herre, kom i Hu, hvad Livet er, til hvilken Tomhed du skabte hvert Menneskebarn!
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
Hvo bliver i Live og skuer ej Død, hvo frelser sin sjæl fra Dødsrigets Hånd? (Sela) (Sheol h7585)
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Hvor er din fordums Nåde, Herre, som du i Trofasthed tilsvor David?
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Kom, Herre, din Tjeners Skændsel i Hu, at jeg bærer Folkenes Spot i min Favn,
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
hvorledes dine Fjender håner, HERRE, hvorledes de håner din Salvedes Fodspor.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
Lovet være HERREN i Evighed, Amen, Amen!

< Zabura 89 >