< Zabura 89 >
1 Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
Ezrakhi Ethan kah Hlohlai BOEIPA kah sitlohnah te, cadilcahma phoeikah cadilcahma duela, kumhal ah ka hlai ni. Namah kah uepomnah te, ka ka neh ka tukkil ni.
2 Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
Sitlohnah loh vaan a khoeng tih, a khuiah na uepomnah na soepboe te kumhal ah ka thui ni.
3 Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
Ka coelh taengah moi ka boh tih ka sal David taengah ka toemngam coeng.
4 cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
Na tiingan te kumhal duela ka thoh vetih na ngolkhoel te cadilcahma phoeikah cadilcahma ham ka hol pah ni. (Selah)
5 Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
Te dongah BOEIPA nang kah khobaerhambae te vaan rhoek loh, na uepomnah khaw a cim hlangping khuiah a uem uh.
6 Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
BOEIPA neh khomong dongah unim aka tluk tih vaan hlang khuiah BOEIPA te u long nim a puet?
7 Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
Pathen taengah tah, boeiping hlangcim kah baecenol nen khaw a sarhing pai. Te dongah a kaepvai boeih lakah a rhih om pai.
8 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
Caempuei Pathen, BOEIPA namah bangla unim aka om? BOEIPA tah tlung tih na kaepvai ah na uepomnah om.
9 Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
Tuitunli kah a hoemdamnah te aka taemrhai khaw namah ni. Tuilae a thoh vaengah amih te na domyok sak.
10 Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
Nang loh Rahab na ngawn bangla na bantha neh na phop tih na thunkha rhoek te na sarhi neh na yaal.
11 Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
Vaan rhoek khaw nang kah, diklai khaw nang kah bal. Lunglai neh anih dongkah aka om boeih namah loh na suen.
12 Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
Tlangpuei neh bantang khaw namah loh na suen. Tabor neh Hermon loh na ming neh tamhoe rhoi.
13 Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
Na ban te thayung thamal sai tih na kut khaw tanglue. Te dongah na bantang kut tah a pomsang.
14 Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
Na ngolkhoel hmuen la duengnah neh tiktamnah om tih sitlohnah neh oltak loh na hmai ah n'doe.
15 Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
BOEIPA kah tamlung aka ming tih na mikhmuh kah vangnah khuiah aka pongpa pilnam tah a yoethen pai saeh.
16 Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
Na ming neh hnin takuem omngaih uh tih na duengnah neh pomsang uh.
17 Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
Amih kah boeimangnah sarhi la nang na om dongah na kolonah neh ka ki khaw na pomsang rhoela na pomsang coeng.
18 Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
BOEIPA tah kaimih kah photling, Israel kah a cim, kaimih kah manghai ni.
19 Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
Saivai atah, na hlangcim rhoek te mangthui neh na voek tih, “Pilnam khui lamkah ka coelh hlangrhalh taengah bomkung ka mop pah tih ka pomsang coeng.
20 Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
Ka sal David te ka hmuh coeng tih kamah kah situi cim neh ka koelh coeng.
21 Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
Ka kut te anih taengah tawn uh tih ka ban loh anih a thoh ni.
22 Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
Anih te thunkha loh phae pawt vetih dumlai ca long khaw phaep mahpawh.
23 Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
Tedae a rhal te anih mikhmuh ah ka phop pah vetih a lunguet khaw ka vuek pah ni.
24 Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
Te vaengah anih taengah kai kah uepomnah neh sitlohnah om vetih ka ming neh a ki khaw pomsang uh ni.
25 Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
A kut te tuitunli soah, a bantang kut te tuiva rhoek soah ka khueh pah ni.
26 Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
Anih loh kai te, “Nang tah ka napa, ka Pathen neh kai ham khangnah lungpang,” lan'khue ni.
27 Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
Kai long khaw anih te caming omthang neh diklai manghai rhoek kah a sangkoek la ka khueh ni.
28 Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
Kamah kah sitlohnah te anih ham kumhal duela ka ngaithuen rhoe ka ngaithuen pah vetih, ka paipi he anih taengah cak ni.
29 Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
Te dongah a tiingan te a yoeyah la ka thoh pah vetih a ngolkhoel loh vaan khohnin bangla om ni.
30 “In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
A ca rhoek loh ka olkhueng he a hnoo uh tih ka tiktamnah dongah a pongpa uh pawt atah,
31 in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
ka khosing te a poeih uh tih ka olpaek te a ngaithuen uh pawt atah,
32 zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
amih kah boekoek te mancai neh, amih thaesainah te khaw tlohthae neh ka cawh thil van ni.
33 amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
Tedae ka sitlohnah he anih taeng lamloh ka phae pah pawt vetih ka uepomnah te rhi ka lat pah mahpawh.
34 Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
Ka paipi he ka poeih pawt vetih ka hmui lamkah aka thoeng khaw ka thovael mahpawh.
35 Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
Ka cimcaihnah neh vai ka toemngam tangtae te David taengah khaw ka laithae mahpawh.
36 cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
Anih kah tiingan te kumhal duela om vetih a ngolkhoel loh kai hmaiah khomik bangla om ni.
37 zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
Hl a bangla kumhal ah cikngae vetih khomong soah uepom laipai la om ni,” na ti. (Selah)
38 Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
Tedae na hlahpham tih na hnawt coeng dongah na koelh hlang te na poe.
39 Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
Na salpa kah paipi te na hai tih a rhuisam khaw diklai neh na poeih pah.
40 Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
Anih kah tanglung khaw boeih na phae pah tih a hmuencak rhoek khaw porhaknah la na khueh pah.
41 Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
Longpuei kah aka pongpa boeih loh anih te a rheth uh dongah a imben rhoek kah kokhahnah coeng.
42 Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
A rhal rhoek kah bantang kut te na pomsang pah tih a thunkha boeih kah ko na hoe sak.
43 Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
A cunghang taeh khaw na kolong pah sak tih caemtloek vaengah khaw na duel pawh.
44 Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
A caihcilnah te na kangkuen sak tih a ngolkhoel te diklai la na voeih pah.
45 Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
A cacawn tue na rhaem pah tih, yah neh na thing. (Selah)
46 Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
BOEIPA nang mevaeng hil nim na thuh uh vetih, na kosi loh hmai bangla a yoeyah la rhong ve?
47 Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
Hlang ca rhoek boeih na suen he a poeyoek mai la. Te dongah mebang khosaknah dongah khaw kai he m'poek lah.
48 Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
Mebang hlang nim aka hing tih dueknah hmuh pawt ham, saelkhui kut lamkah a hinglu te aka poeng aka hal thai? (Selah) (Sheol )
49 Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
Ka Boeipa aw, lamhma kah na sitlohnah te ta? David taengah na uepomnah neh na toemngam te.
50 Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
Ka Boeipa aw na sal sokah kokhahnah he poek lah. Pilnam kah tuituknah boeih he ka kodang ah ka phueih he.
51 zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
BOEIPA aw, na thunkha rhoek loh m'veet uh coeng te, na koelh hlang kah kholaeh khaw a veet uh coeng te.
52 Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!
BOEIPA tah kumhal duela a yoethen pai. Amen phoeiah Amen.