< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Korahoğulları'nın mezmuru - İlahi - Müzik şefi için - “Mahalat Leannot” makamında - Ezrahlı Heman'ın Maskili Ya RAB, beni kurtaran Tanrı, Gece gündüz sana yakarıyorum.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Duam sana erişsin, Kulak ver yakarışıma.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
Çünkü sıkıntıya doydum, Canım ölüler diyarına yaklaştı. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Ölüm çukuruna inenler arasında sayılıyorum, Tükenmiş gibiyim;
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Ölüler arasına atılmış, Artık anımsamadığın, İlginden yoksun, Mezarda yatan cesetler gibiyim.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Beni çukurun dibine, Karanlıklara, derinliklere attın.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Öfken üzerime çöktü, Dalga dalga kızgınlığınla beni ezdin. (Sela)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Yakınlarımı benden uzaklaştırdın, İğrenç kıldın beni gözlerinde. Kapalı kaldım, çıkamıyorum.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Üzüntüden gözlerimin feri sönüyor, Her gün sana yakarıyorum, ya RAB, Ellerimi sana açıyorum.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Harikalarını ölülere mi göstereceksin? Ölüler mi kalkıp seni övecek? (Sela)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Sevgin mezarda, Sadakatin yıkım diyarında duyurulur mu?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Karanlıklarda harikaların, Unutulmuşluk diyarında doğruluğun bilinir mi?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Ama ben, ya RAB, yardıma çağırıyorum seni, Sabah duam sana varıyor.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Niçin beni reddediyorsun, ya RAB, Neden yüzünü benden gizliyorsun?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Düşkünüm, gençliğimden beri ölümle burun burunayım, Dehşetlerinin altında tükendim.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Şiddetli gazabın üzerimden geçti, Saçtığın dehşet beni yedi bitirdi.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Bütün gün su gibi kuşattılar beni, Çevremi tümüyle sardılar.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Eşi dostu benden uzaklaştırdın, Tek dostum karanlık kaldı.