< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Canción de Salmo: a los hijos de Coré: al Vencedor: para cantar sobre Mahalat; Masquil de Hemán el ezraíta. Oh SEÑOR, Dios de mi salud, día y noche clamo delante de ti.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Entre mi oración en tu presencia; inclina tu oído a mi clamor.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
Porque mi alma está harta de males, y mi vida ha llegado a la sepultura. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Soy contado con los que descienden al hoyo, soy como hombre sin fuerza;
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
librado entre los muertos. Como los muertos que duermen en el sepulcro, que no te acuerdas más de ellos, y que son cortados de tu mano.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Me has puesto en el hoyo profundo, en tinieblas, en honduras.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Sobre mí se ha acostado tu ira, y me has afligido con todas tus ondas. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Has alejado de mí mis conocidos; me has puesto por abominación a ellos; estoy encerrado, y no saldré.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mis ojos enfermaron a causa de mi aflicción; te he llamado, oh SEÑOR, cada día he extendido a ti mis manos.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
¿Harás tú milagro a los muertos? ¿Se levantarán los muertos para alabarte? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
¿Será contada en el sepulcro tu misericordia, o tu verdad en la perdición?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
¿Será conocida en las tinieblas tu maravilla, y tu justicia en la tierra del olvido?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Mas yo a ti he clamado, oh SEÑOR; y de mañana te previno mi oración.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
¿Por qué, oh SEÑOR, desechas mi alma? ¿Por qué escondes tu rostro de mí?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Yo soy pobre y menesteroso; desde la juventud he llevado tus temores, he estado medroso.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Sobre mí han pasado tus iras; tus espantos me han cortado.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Me han rodeado como aguas de continuo; me han cercado a una.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Has alejado de mí al amigo y al compañero; y mis conocidos has puesto en la tiniebla.