< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Oh Yavé, ʼElohim de mi salvación, Día y noche clamo delante de Ti.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Llegue mi oración a tu Presencia. Inclina tu oído a mi clamor.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
Porque mi alma está harta de aflicciones, Y mi vida se acerca al Seol. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Soy contado entre los que descienden al sepulcro. Soy como un varón sin fuerza,
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Olvidado entre los muertos, Como los asesinados que están tendidos en la tumba, De quienes ya no te acuerdas, y son cortados de tu mano.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Me colocaste en la fosa más profunda, En lugares oscuros, en las profundidades.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Tu ira pesa sobre mí. Me afliges con todas tus olas. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Alejaste a mis conocidos de mí. Me pusiste como un objeto de repugnancia para ellos. Estoy encerrado y no puedo salir.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mis ojos se enfermaron por causa de la aflicción. Cada día te invoco, oh Yavé. Extiendo mis manos hacia Ti:
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
¿Harás milagros a favor de los muertos? ¿Se levantarán los muertos para alabarte? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
¿Se anunciará en el sepulcro tu misericordia, Tu fidelidad en el Abadón?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
¿Serán reconocidas tus maravillas en la oscuridad, Y tu justicia en la tierra del olvido?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Pero yo te invoco, oh Yavé, Clamo por ayuda. De mañana mi súplica llega delante de Ti.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
¿Por qué, oh Yavé, desechas mi alma? ¿Por qué escondes de mí tu rostro?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Desde mi juventud estuve afligido y necesitado. Sufrí tus terrores. Estuve turbado.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Tu ardiente ira pasó sobre mí. Tus terrores me destruyeron.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Me rodean de continuo como aguas. En conjunto me cercaron.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Alejaste de mí a mis amigos y compañeros. Solo la oscuridad es mi compañera.

< Zabura 88 >