< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Una canción. Un salmo de los descendientes de Coré. Para el director del coro. Al son de “Mahalath Leannoth”. Un masquil por Hemán el ezraíta Señor, Dios de mi salvación, clamo a ti de día y de noche.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Por favor escucha mi oración; escucha mis palabras de súplica.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
Mi vida está llena de problemas, y mi muerte se acerca. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Soy contado entre los moribundos; un hombre sin fuerzas.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Soy abandonado entre los muertos, tendido como un cadáver en la tumba, olvidado y dejado a tu cuidado.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Me has puesto en un pozo profundo, entre las penumbras.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Tu hostilidad me maltrata; me estás ahogando entre tus olas abrumadoras. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Has hecho que mis enemigos me eviten, haciéndome repulsivo a sus vistas. Estoy atrapado, no puedo huir.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Señor, he llorado suplicándote cada día por ayuda, extendiendo mis manos hacia ti.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
¿Haces milagros entre los muertos? ¿Se levantan los muertos para alabarte? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Tu gran amor, ¿Se menciona en la tumba? Tu fidelidad, ¿Es discutida en lugar de destrucción?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
¿Las cosas maravillosas que haces son conocidas en las tinieblas? ¿Tu bondad es conocida en la tierra del olvido?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Pero clamo a ti pidiendo ayuda; cada mañana oro a ti.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Señor, ¿Por qué me rechazas? ¿Por qué te alejas de mí?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
He estado enfermo desde que era joven, a menudo estuve a las puertas de la muerte. He tenido que soportar las cosas terribles que me has hecho. ¡Estoy desesperado!
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Tu ira me ha vencido; las cosas terribles que haces me han destruido.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Ellos me rodean constantemente como aguas de una inundación, succionándome.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Has hecho que mi familia y mis amigos se alejen. La oscuridad es mi única amiga.