< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Cântico e Salmo dos filhos de Coré, para o regente, conforme “Maalate Leanote”. Instrução feita por Hemã, o Ezraíta: Ó SENHOR Deus de minha salvação, dia [e] noite clamo diante de ti.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Que minha oração chegue à tua presença; inclina os teus ouvidos ao meu clamor.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
Porque minha alma está cheia de aflições, e minha vida se aproxima do Xeol. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Já estou contado entre os que descem à cova; tornei-me um homem sem forças.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Abandonado entre os mortos, como os feridos de morte que jazem na sepultura, aos quais tu já não te lembra mais, e já estão cortados [para fora do poder] de tua mão.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Puseste-me na cova mais profunda, nas trevas [e] nas profundezas.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
O teu furor pesa sobre mim, e [me] oprimiste com todas as tuas ondas. (Selá)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Afastaste de mim os meus conhecidos, fizeste-me abominável para com eles; estou preso, e não posso sair.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Meus olhos estão fracos por causa da opressão; clamo a ti, SENHOR, o dia todo; a ti estendo minhas mãos.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Farás tu milagres aos mortos? Ou mortos se levantarão, e louvarão a ti? (Selá)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Tua bondade será contada na sepultura? Tua fidelidade na perdição?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Serão conhecidas tuas maravilhas nas trevas? E tua justiça na terra do esquecimento?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Porém eu, SENHOR, clamo a ti; e minha oração vem ao teu encontro de madrugada.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Por que tu, SENHOR, rejeitas minha alma, e escondes tua face de mim?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Tenho sido afligido e estou perto da morte desde a minha juventude; tenho sofrido teus temores, e estou desesperado.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Os ardores de tua ira têm passado por mim; teus terrores me destroem.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Rodeiam-me como águas o dia todo; cercam-me juntos.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Afastaste de mim meu amigo e meu companheiro; meus conhecidos [estão em] trevas.

< Zabura 88 >