< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Éternel, Dieu de ma délivrance, je crie jour et nuit devant toi.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Que ma prière parvienne en ta présence; incline ton oreille à mon cri.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
Car mon âme est rassasiée de maux, et ma vie touche au séjour des morts. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Je suis compté parmi ceux qui descendent dans la fosse; je suis comme un homme sans vigueur,
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Gisant parmi les morts, tel que les blessés à mort, qui sont couchés dans le tombeau, dont tu ne te souviens plus, et qui sont séparés de ta main.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Tu m'as mis dans la fosse la plus basse, dans les lieux ténébreux, dans les abîmes.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Ta colère pèse sur moi, et tu m'accables de tous tes flots. (Sélah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Tu as éloigné de moi ceux que je connais; tu m'as rendu pour eux un objet d'horreur; je suis enfermé et je ne puis sortir.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mon œil se consume par l'affliction; je t'invoque, ô Éternel, tous les jours; j'étends mes mains vers toi.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Feras-tu quelque merveille pour les morts? Ou les trépassés se lèveront-ils pour te louer? (Sélah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Annoncera-t-on ta bonté dans le tombeau, et ta fidélité dans l'abîme?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Connaîtra-t-on tes merveilles dans les ténèbres, et ta justice dans la terre d'oubli?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Et moi, Éternel, je crie à toi; ma prière te prévient dès le matin.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Éternel, pourquoi rejettes-tu mon âme, et me caches-tu ta face?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Je suis affligé et comme expirant dès ma jeunesse; je suis chargé de tes terreurs, je suis éperdu.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Tes fureurs ont passé sur moi; tes épouvantes me tuent.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Elles m'environnent comme des eaux chaque jour; elles m'enveloppent toutes à la fois.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Tu as éloigné de moi amis et compagnons; ceux que je connais, ce sont les ténèbres.