< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Maskil d'Héman Ezrahite, [qui est] un Cantique de Psaume, [donné] au maître chantre d'entre les enfants de Coré, [pour le chanter] sur Mahalath-lehannoth. Eternel! Dieu de ma délivrance, je crie jour et nuit devant toi.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Que ma prière vienne en ta présence; ouvre ton oreille à mon cri.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
Car mon âme a tout son saoul de maux, et ma vie est venue jusqu'au sépulcre. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
On m'a mis au rang de ceux qui descendent en la fosse; je suis devenu comme un homme qui n'a plus de vigueur;
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Placé parmi les morts, comme les blessés à mort couchés au sépulcre, desquels il ne te souvient plus, et qui sont retranchés par ta main.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Tu m'as mis en une fosse des plus basses, dans des lieux ténébreux, dans des lieux profonds.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Ta fureur s'est jetée sur moi, et tu m'as accablé de tous tes flots; (Sélah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Tu as éloigné de moi ceux de qui j'étais connu, tu m'as mis en une extrême abomination devant eux; je suis enfermé tellement, que je ne puis sortir.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mon œil languit d'affliction; Eternel! je crie à toi tout le jour, j'étends mes mains vers toi.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Feras-tu un miracle envers les morts? ou les trépassés se relèveront-ils pour te célébrer? (Sélah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Racontera-t-on ta miséricorde dans le sépulcre? [et] ta fidélité dans le tombeau?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Connaîtra-t-on tes merveilles dans les ténèbres; et ta justice au pays d'oubli?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Mais moi, ô Eternel! je crie à toi, ma prière te prévient dès le matin.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Eternel! pourquoi rejettes-tu mon âme, pourquoi caches-tu ta face de moi?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
Je suis affligé et comme rendant l'esprit dès ma jeunesse; j'ai été exposé à tes terreurs, et je ne sais où j'en suis.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Les ardeurs de ta [colère] sont passées sur moi, et tes frayeurs m'ont retranché.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Ils m'ont tout le jour environné comme des eaux, ils m'ont entouré tous ensemble.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Tu as éloigné de moi mon ami, même mon intime ami, et ceux de qui je suis connu me sont des ténèbres.

< Zabura 88 >