< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
A Song [or] Psalm for the sons of Korah, to the chief Musician upon Mahalath Leannoth, Maschil of Heman the Ezrahite. O LORD God of my salvation, I have cried day [and] night before thee:
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Let my prayer come before thee: incline thy ear to my cry;
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
For my soul is full of troubles: and my life draweth nigh to the grave. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I am counted with them that go down into the pit: I am as a man [that hath] no strength:
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Free among the dead, like the slain that lie in the grave, whom thou rememberest no more: and they are cut off from thy hand.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Thou hast laid me in the lowest pit, in darkness, in the deeps.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Thy wrath lieth hard upon me, and thou hast afflicted [me] with all thy waves. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Thou hast put away my acquaintance far from me; thou hast made me an abomination to them: [I am] shut up, and I cannot come forth.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
My eye mourneth by reason of affliction: LORD, I have called daily upon thee, I have stretched out my hands to thee.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Wilt thou show wonders to the dead? shall the dead arise [and] praise thee? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Shall thy loving-kindness be declared in the grave? [or] thy faithfulness in destruction?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Shall thy wonders be known in the dark? and thy righteousness in the land of forgetfulness?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
But to thee have I cried, O LORD; and in the morning shall my prayer come before thee.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
LORD, why castest thou off my soul? [why] hidest thou thy face from me?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
I [am] afflicted and ready to die from [my] youth up: [while] I suffer thy terrors I am distracted.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Thy fierce wrath goeth over me; thy terrors have cut me off.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
They came around me daily like water; they encompassed me together.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Lover and friend hast thou put far from me, [and] my acquaintance into darkness.

< Zabura 88 >