< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
A Song, a psalm of the Korahites. To the leader: according to Mahalath Leannoth. A Maskil of Heman the Ezrahite. O Lord my God, I cry for help in the day-time, in the night my cry is before you;
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
let my prayer come into your presence, incline your ear to my cry.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
For I am sated with sorrow, my life draws near to Sheol. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I am counted with those who go down to the pit; without strength am I.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
My home is among the dead, like the slain that lie in the grave, whom you remember no more cut off as they are from your hand.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
In the deepest pit you have put me, in shadows deep and dark.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Your wrath lies heavy upon me, waves of your anger roll over me. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
You have put my friends far from me, you have made them shun me. I am shut in, and cannot escape,
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
my eyes are wasted with sorrow. I call on you, Lord, every day, spreading my hands out to you.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
For the dead can you work wonders? Can the shades rise again to praise you? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Can your kindness be told in the grave, your faithfulness in the tomb?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Can your wonders be known in the darkness, or your help in the land of forgetfulness?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
I cry for help to you, in the morning my prayer comes before you.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Why, O Lord, do you spurn me, and hide your face from me?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
From my youth I am wretched and dying, I am numbed by the terrors I bear.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
The fires of your wrath have passed over me, your terrors destroy me,
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
surging around me forever, hemming me in altogether.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Those who love me you put far from me; the dark is my only friend.

< Zabura 88 >