< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
“A psalm of the sons of Korah. For the leader of the music. Upon wind instruments. A psalm of Heman, the Ezrahite.” O LORD, God of my salvation! To thee do I cry by day, And by night is my prayer before thee!
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Let my supplication come before thee; Incline thine ear to my cry!
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
For my soul is full of misery, And my life draweth near to the underworld. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I am counted with those who are going down to the pit; I am like one who hath no strength.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
I am left to myself among the dead, Like the slain who lie in the grave, Whom thou no more rememberest, And who are cut off from thy [[protecting]] hand.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Thou hast placed me in a deep pit, In a dark and deep abyss.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Thy wrath presseth hard upon me, And thou afflictest me with all thy waves! (Pause)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Thou hast put mine acquaintances far from me, Yea, thou hast made me their abhorrence: I am shut up, and cannot go forth.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mine eyes languish by reason of my affliction. I call upon thee daily, O LORD! To thee do I stretch out my hands!
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Canst thou show wonders to the dead? Shall the dead arise, and praise thee? (Pause)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Shall thy goodness be declared in the grave, Or thy faithfulness in the place of corruption?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Shall thy wonders be known in the dark, And thy justice in the land of forgetfulness?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
To thee do I cry, O LORD! In the morning doth my cry come before thee.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Why, O LORD! dost thou cast me off? Why hidest thou thy face from me?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
I have been afflicted and languishing from my youth; I suffer thy terrors, and am distracted.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Thy fierce wrath overwhelmeth me; Thy terrors utterly destroy me.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
They surround me daily like water; They compass me about together.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Lover and friend hast thou put far from me; My acquaintances are withdrawn from my sight.

< Zabura 88 >