< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
A SONG. A PSALM OF THE SONS OF KORAH. TO THE OVERSEER. [SET] ON “SICKNESS TO AFFLICT.” AN INSTRUCTION OF HEMAN THE EZRAHITE. O YHWH, God of my salvation, Daily I have cried, nightly before You,
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
My prayer comes in before You, Incline Your ear to my loud cry,
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
For my soul has been full of evils, And my life has come to Sheol. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I have been reckoned with those going down [to] the pit, I have been as a man without strength.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Among the dead—free, As pierced ones lying in the grave, Whom You have not remembered anymore, Indeed, they have been cut off by Your hand.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
You have put me in the lowest pit, In dark places, in depths.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Your fury has lain on me, And You have afflicted [with] all Your breakers. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
You have put my acquaintance far from me, You have made me an abomination to them, Shut up—I do not go forth.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
My eye has grieved because of affliction, I called You, O YHWH, all the day, I have spread out my hands to You.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Do You do wonders to the dead? Does Rephaim rise? Do they thank You? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Is Your kindness recounted in the grave? Your faithfulness in destruction?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Are Your wonders known in the darkness? And Your righteousness in the land of forgetfulness?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
And I, to You, O YHWH, I have cried, And in the morning my prayer comes before You.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Why, O YHWH, do You cast off my soul? You hide Your face from me.
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
I [am] afflicted, and expiring from youth, I have borne Your terrors—I pine away.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Your wrath has passed over me, Your terrors have cut me off,
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
They have surrounded me as waters all the day, They have gone around against me together,
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
You have put lover and friend far from me, My acquaintance [is] the place of darkness!