< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
A canticle of a psalm for the sons of Core: unto the end, for Maheleth, to answer understanding of Eman the Ezrahite. O Lord, the God of my salvation: I have cried in the day, and in the night before thee.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Let my prayer come in before thee: incline thy ear to my petition.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
For my soul is filled with evils: and my life hath drawn nigh to hell. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I am counted among them that go down to the pit: I am become as a man without help,
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Free among the dead. Like the slain sleeping in the sepulchres, whom thou rememberest no more: and they are cast off from thy hand.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
They have laid me in the lower pit: in the dark places, and in the shadow of death.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Thy wrath is strong over me: and all thy waves thou hast brought in upon me.
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Thou hast put away my acquaintance far from me: they have set me an abomination to themselves. I was delivered up, and came not forth:
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
My eyes languished through poverty. All the day I cried to thee, O Lord: I stretched out my hands to thee.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Wilt thou shew wonders to the dead? or shall physicians raise to life, and give praise to thee?
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Shall any one in the sepulchre declare thy mercy: and thy truth in destruction?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Shall thy wonders be known in the dark; and thy justice in the land of forgetfulness?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
But I, O Lord, have cried to thee: and in the morning my prayer shall prevent thee.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Lord, why castest thou off my prayer: why turnest thou away thy face from me?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
I am poor, and in labours from my youth: and being exalted have been humbled and troubled.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Thy wrath hath come upon me: and thy terrors have troubled me.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
They have come round about me like water all the day: they have compassed me about together.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Friend and neighbour thou hast put far from me: and my acquaintance, because of misery.

< Zabura 88 >