< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
A song of a Psalm for the sons of Core for the end, upon Maeleth for responsive [strains], of instruction for Aeman the Israelite. O Lord God of my salvation, I have cried by day and in the night before thee.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Let my prayer come in before thee; incline thine ear to my supplication, O Lord.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
For my soul is filled with troubles, and my life has drawn nigh to Hades. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I have been reckoned with them that go down to the pit; I became as a man without help;
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
free among the dead, as the slain ones cast out, who sleep in the tomb; whom thou rememberest no more; and they are rejected from thy hand.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
They laid me in the lowest pit, in dark [places], and in the shadow of death.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Thy wrath has pressed heavily upon me, and thou hast brought upon me all thy billows. (Pause)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Thou hast removed my acquaintance far from me; they have made me an abomination to themselves; I have been delivered up, and have not gone forth.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mine eyes are dimmed from poverty; but I cried to thee, O Lord, all the day; I spread forth my hands to thee.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Wilt thou work wonders for the dead? or shall physicians raise [them] up, that they shall praise thee?
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Shall any one declare thy mercy in the tomb? and thy truth in destruction?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Shall thy wonders be known in darkness? and thy righteousness in a forgotten land?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
But I cried to thee, O Lord; and in the morning shall my prayer prevent thee.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Wherefore, O Lord, dost thou reject my prayer, [and] turn thy face away from me?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
I am poor and in troubles from my youth; and having been exalted, I was brought low and into despair.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Thy wrath has passed over me; and thy terrors have greatly disquieted me.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
They compassed me like water; all the day they beset me together.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Thou hast put far from me [every] friend, and mine acquaintances because of [my] wretchedness.