< Zabura 88 >
1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
A song. A Psalm of the sons of Korah. For the choirmaster. According to Mahalath Leannoth. A Maskil of Heman the Ezrahite. O LORD, the God of my salvation, day and night I cry out before You.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
May my prayer come before You; incline Your ear to my cry.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
For my soul is full of troubles, and my life draws near to Sheol. (Sheol )
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
I am counted among those descending to the Pit. I am like a man without strength.
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
I am forsaken among the dead, like the slain who lie in the grave, whom You remember no more, who are cut off from Your care.
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
You have laid me in the lowest Pit, in the darkest of the depths.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
Your wrath weighs heavily upon me; all Your waves have submerged me.
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
You have removed my friends from me; You have made me repulsive to them; I am confined and cannot escape.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
My eyes grow dim with grief. I call to You daily, O LORD; I spread out my hands to You.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
Do You work wonders for the dead? Do departed spirits rise up to praise You?
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
Can Your loving devotion be proclaimed in the grave, Your faithfulness in Abaddon?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
Will Your wonders be known in the darkness, or Your righteousness in the land of oblivion?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
But to You, O LORD, I cry for help; in the morning my prayer comes before You.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Why, O LORD, do You reject me? Why do You hide Your face from me?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
From my youth I was afflicted and near death. I have borne Your terrors; I am in despair.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
Your wrath has swept over me; Your terrors have destroyed me.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
All day long they engulf me like water; they enclose me on every side.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
You have removed my beloved and my friend; darkness is my closest companion.