< Zabura 87 >

1 Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
Синів Коре́євих. Псалом, Пісня.
2 Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
Госпо́дь любить брами Сіону понад усі се́лища Яковові.
3 Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
Славне розповіда́ють про тебе, місто Боже! (Се́ла)
4 “Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
„Тим, хто знає мене, нагадаю про Ра́гав та про Вавило́н; ось Филисте́я та Тир з Ку́шем кажуть: Отой народився був там“.
5 Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
І про Сіон говори́тимуть: „Той і той народився був у ньому, й Сам Всевишній зміцняє його́“!
6 Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
Господь буде лічити у книзі наро́дів: „Оцей народився був там“! (Се́ла)
7 Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”
І співають, і грають вони: „У Тобі — всі джере́ла мої!“

< Zabura 87 >